ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Tarwatsa Ofishin ‘Yansanda, Sun Kashe ‘Yansanda 3 A Anambra

by Sadiq
4 years ago
Anambra

Wasu ‘yan bindiga da suka kai harin bam a ofishin ‘yansanda na Ogidi da ke karamar hukumar Idemili ta Arewa a Jihar Anambra, sun kashe ‘yansanda uku.

LEADERSHIP ta samu labarin cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Asabar.

  • An Gurfanar Da Sojoji 68 A Gaban Kotu Kan Zargin Rashin Da’a A Sokoto
  • Ilimin Taurari Zai Iya Warware Matsalolin Da Kasar Nan Ke Fuskanta –Shaikh Muhajjadina

Majiyoyi a yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun far wa ofishin ‘yansandan inda suka dinga harbi ko ina sannan suka jefa bama-bamai cikin ofishin inda suka kone ginin.

ADVERTISEMENT

Kakakin ‘yansandan Jihar, DSP Ikenga Tochukwu, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce an tura tawagar ‘yansanda domin dawo da tsaro a yankin.

Ya ce, “Rundunar ‘yansandan Jihar Anambra ta kara karfafa tsaro a yankin Idemili na Arewa da ke jihar, biyo bayan harin da aka kai wa rundunar ‘yansandan yankin Ogidi da sanyin safiyar yau, inda ‘yansanda uku suka rasa rayukansu.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

“Yan bindigar sun fara harbe-harbe kan rundunar ‘yansandan, sannan sun jefa bama-bamai.

DSP Tochukwu ya kara da cewa baya ga ‘yansandan uku da aka kashe, an kone ofishin ‘yansandan.

Ya kara da cewa: “Rundunar ta damu da asarar rayuka da dukiya sakamakon wannan harin.”

Ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankali tare da tabbatar da cewa kwamishinan ‘yansanda, CP Echeng Echeng, ya jajirce wajen hana wadannan miyagu ci gaba da kai hare-hare.

Ya bayyana cewa, CP Echeng ya kara daukar matakai na inganta tsaro da rayuka da dukiyoyi a jihar, inda ya ce tuni aka fara tantance harin da aka kai ofishin ‘yansanda na Ogidi.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Abin Da Ya Sa Zan Yi Tattaki Daga Neja Zuwa Abuja Idan Atiku Ya Ci – Aminu Hassan

Abin Da Ya Sa Zan Yi Tattaki Daga Neja Zuwa Abuja Idan Atiku Ya Ci - Aminu Hassan

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Anambra

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Anambra

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.