Mustapha Ibrahim">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

’Yan Kwankwasiyya Sun Fara Sansana Hon. Sharada A Wajen Ta’aziyyar Mahaifin Kwankwaso

by Mustapha Ibrahim
December 31, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Alhaji Musa Sale Kwankwaso
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tun ranar Juma’a da ta gabata da Allah ya karbi ran Hakimin Madobi kuma Makaman a Masarautar Karaye, Alhaji Musa Sale Kwankwaso, wanda kuma mahaifi ne ga tsohon Gwamnan Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, jama’a, manya, shugabanni da ’yan kasuwa, malamai da sarakuna, jami’an gwamnati da sauran al’umma daga ko’ina cikin Nijeriya har da makota ke tururuwa zuwa ta’a ziyya da jajenta wa Madugun na Kwankwasiyya.

Sai dai ziyarar da Hon. Sha’aban Ibrahim Sharada, dan Majalisar Wakilai a Majalisar Tarayya ta Abuja daga karamar hukumar Birnin Kano a jam’iyar APC kuma makusanci na hannun daman Shugaban Kasa Muhammad Buhari ziyarar ta’aziyar ta Sharada ta dauki hankalin duniya kan irin gagarumar tarba da mabiya Kwankwasiyya karkashin Sanata Kwankwaso su ka yi ma sa duka da kasancewarsa dan jam’iyyar APC a wannan lokaci.

samndaads

Shi ma a jawabinsa Hon Sha’aban Ibrahim Sharada ya nuna farin cikinsa da irin tarbar da a ka yi ma sa a gidan Sanata Kwankwaso da ke Milla Road, inda a ke zamam makokin na Makaman Karaye da ya rasu, inda Sha’aban ya nuna gamsuwasa da akidar cigaba irin ta Madugun Kwankwasiyya da mabiyansa na yin adalci ga kowa da siyasa bada gaba ba.

Tuni dai Mataimakin Gwamnan Kano Dr Nasiru Yusuf Gawuna, da wazirin Masarautar Gaya Dattijo kuma sakataran Gwamnatin Kano Alhaji Usman Alhaji su ka jagoranci wani ayari na jami’an Gwamnatin Kano dan ziyarar ta’a ziya ga Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso kan rashin da akayi masa a wanan lokaci a madadin Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje haka shi ma mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayaro SAN KANO inda kuma su kayi adu’a ta Neman rahama da gafara ga Marigayi da kuma ba Sanata Rabi’u hakuri da sauran iyalan kan rashin makaman karaye wanda ya kwanta dama a Ranar Juma’a da ta gabata.

SendShareTweetShare
Previous Post

Za Mu Farfado Da Darajar Makarantar Firamaren ’Ya’yan Ma’Aikatan BUK – Umar Bala

Next Post

Akwai Bukatar Yin Koyi Da Kungiyar Tsofaffin Dalibain Kwalli Aji Na 75 – Alkali Faruk

RelatedPosts

Sojoji Sun Tarwatsa Sansanin Boko Haram A Borno 

by Mustapha Ibrahim
15 hours ago
0

Rundunar sojan Najeriya ta bayyana samun nasarar tarwatsa sansanin da...

Jam'iyyar Adawa

Jam’iyyar Adawa Ta PDP Ta Yi Babban Kamu A Kebbi

by Mustapha Ibrahim
15 hours ago
0

Jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Kebbi tayi babban kamu...

Majalisar Malamai

Majalisar Malamai A Kogi Ta Raba Zakkar Miliyan N2.5 Ga Mutum 63

by Mustapha Ibrahim
15 hours ago
0

Majalisar Malamai ta Najeriya,reshen jihar Kogi(Council of Ulama) ta rarraba...

Next Post
Alkali Faruk

Akwai Bukatar Yin Koyi Da Kungiyar Tsofaffin Dalibain Kwalli Aji Na 75 – Alkali Faruk

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version