• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa Sun Nemi Yanke Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Karya Dokar Zabe

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin tsaftace harkokin zabe a Nijeriya, ‘yan majalisar wakilai sun gabatar da kuduri na samar da hukunci mai tsanani ga masu karya dokar zabe.

A ranar 23 ga watan Agustan 2023, ‘yan majalisar wakilai sun gudanar da zaman jin ra’ayoyin jama’a, domin samun amincewar masu ruwa da tsaki na neman samar da hukunci mai tsanani ga masu karya dokar zabe.

  • Mace Za Ta Iya Yin Limancin Sallah?
  • Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wani Masallaci Ya Kashe Akalla Mutane 18 A Afganistan

Rikici na daya daga cikin abubuwan da ke damun zaben kasar nan wanda ke tarwatsa lamura gabanin zabe da kuma bayan gudanar da zabe.

Dalilan da suke haddasa rikici shi ne bambanci. Irin wadannan laifuka ana amfani da su a wajen abokan takara ko wajen yin mugudi a lokacin zabe.

‘Yan siyasa suna biyan wakilansu wajen yin kalamun batanci ko daukan nauyin ‘yan daba domin farmakar runfar zabe ko sace akwati ko lalata takardun zabe ko sayan kuri’u ko yin garkuwa ko kashe abokan takara da magoya bayansu.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Tun kafin babban zaben 2023, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fara fadakarwa.

Amma abun takaicin shi ne, a cikin dokar zaben da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya rattaba hannu a watannin da suka gabata ta kasa samar da tsauraren hukunci da za a yi wa wadanda suka karya dokar zabe.

Domin kawo karshen rikicin zabe, ‘yan majalisa sun samar da kudurin dokar hukunta masu karya dokar zabe wanda ya tsallake karatu na farko da na biyu, inda har ya kai da sauraron jin ra’ayoyin jama’a a kan kudurin.

A wurin zaman jin ra’ayoyin jama’a, Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ya nuna goyon bayansa ga kudurin, wanda ya bayyana cewa lokacin da kudurin ya zama doka, hukumarsa za ta samu kunciyar hankali na tabbatar da an hukunta wadanda suka karya dokar zabe, musamman muyagun ‘yan siyasa masu daukar nauyin ‘yan daba wajen tayar da zaune-tsaye.

A cewarsa, sake fasalin harkokin zabe ba zai yuwu ba har sai an hukunta wadanda suke karya dokar zabe.

Yakubu ya kara da cewa hukumar INEC tana da nauyi masu yawa da suka rataya a wuyanta ciki har da gurfanar da masu karya dokar zabe duk da irin kalubalen da hukumar ke fuskanta.

Ya ce tun daga zaben 2015, sun samu laifuka guda 125 game da karya dokar zabe a kotuna mabambanta, amma masu laifi 60 aka iya hukuntawa.

Tun da farko da yake gabatar da kudurin a zauren majalisa, shugaban majalisar wakilai, Hon. Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa rikicin zabe yana janyo karancin inganci da cin hanci da rashawa da rikicin shugabanci, wanda suke taimakawa wajen magudin zabe ta yadda masu laifi suke iya juya gwamnati sabani tsarin dimokuradiyya.

Gbajabiamila wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Hon. Idris Wase ya ce ko shakka babu akwai bukatar yin aiki sosai wajen tsaftace kasar nan daga rikicin zabe da karya dokar zabe.

Kudurin dokar na shafi 19 ya tanadi hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari ga duk wanda aka samu da tsoma baki da taka rawa wajen bayar da rashawa kan zabe.

Sanna sashe na 26 ya tanadi hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari ko tarar naira 40,000, 000 ga duk wanda aka kama da kwacewa ko lalata takardun zabe ko kuma duk wani kundi da ya shafi zabe.

Haka ma sashi na 32 na kudurin dokar ya tanadi hukuncin daurin shekaru 10 ko tarar naira miliyan 40 ga masu kalammun batanci a kan zabe.

Hakazalika, kudurin dokar na shafi 13 ya tanadi hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari ko tarar naira 3,000,000 ga duk wanda aka samu da magudin zabe ko bayar da jawaban karya lokacin da INEC take bayar da katin zabe.

Sannan sashi na 25 ya tanadi hukuncin daurin shekaru biyar ko tarar naira 10,000,000 ga wanda ya lika fostan yakin neman zabe a gida ko a shago ba tare da sanin mai wurin ba, da dai sauran sashi da suka tanadi hukunci ga masu karya dokar zabe.

Idan majalisa ta dawo daga hutu a ranar 20 ga watan Satumbar 2022, za a gudanar da karatu na uku game da wannan kuduri tare da tura kudurin ga majalisar dattawa kafin gabatar wa shugaban kasa domin ya rattaba hannu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan MajalisaDokar ZabeHukunciKarya
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane Da Dama A Masallacin Juma’a A Zamfara

Next Post

‘Yan Fashi Sun Yi Wa Aubameyang Sata A Gidansa

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
‘Yan Fashi Sun Yi Wa Aubameyang Sata A Gidansa

‘Yan Fashi Sun Yi Wa Aubameyang Sata A Gidansa

LABARAI MASU NASABA

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.