• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa Sun Nemi Yanke Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Karya Dokar Zabe

by Yusuf Shuaibu
3 years ago

A kokarin tsaftace harkokin zabe a Nijeriya, ‘yan majalisar wakilai sun gabatar da kuduri na samar da hukunci mai tsanani ga masu karya dokar zabe.

A ranar 23 ga watan Agustan 2023, ‘yan majalisar wakilai sun gudanar da zaman jin ra’ayoyin jama’a, domin samun amincewar masu ruwa da tsaki na neman samar da hukunci mai tsanani ga masu karya dokar zabe.

  • Mace Za Ta Iya Yin Limancin Sallah?
  • Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wani Masallaci Ya Kashe Akalla Mutane 18 A Afganistan

Rikici na daya daga cikin abubuwan da ke damun zaben kasar nan wanda ke tarwatsa lamura gabanin zabe da kuma bayan gudanar da zabe.

Dalilan da suke haddasa rikici shi ne bambanci. Irin wadannan laifuka ana amfani da su a wajen abokan takara ko wajen yin mugudi a lokacin zabe.

‘Yan siyasa suna biyan wakilansu wajen yin kalamun batanci ko daukan nauyin ‘yan daba domin farmakar runfar zabe ko sace akwati ko lalata takardun zabe ko sayan kuri’u ko yin garkuwa ko kashe abokan takara da magoya bayansu.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Tun kafin babban zaben 2023, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fara fadakarwa.

Amma abun takaicin shi ne, a cikin dokar zaben da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya rattaba hannu a watannin da suka gabata ta kasa samar da tsauraren hukunci da za a yi wa wadanda suka karya dokar zabe.

Domin kawo karshen rikicin zabe, ‘yan majalisa sun samar da kudurin dokar hukunta masu karya dokar zabe wanda ya tsallake karatu na farko da na biyu, inda har ya kai da sauraron jin ra’ayoyin jama’a a kan kudurin.

A wurin zaman jin ra’ayoyin jama’a, Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ya nuna goyon bayansa ga kudurin, wanda ya bayyana cewa lokacin da kudurin ya zama doka, hukumarsa za ta samu kunciyar hankali na tabbatar da an hukunta wadanda suka karya dokar zabe, musamman muyagun ‘yan siyasa masu daukar nauyin ‘yan daba wajen tayar da zaune-tsaye.

A cewarsa, sake fasalin harkokin zabe ba zai yuwu ba har sai an hukunta wadanda suke karya dokar zabe.

Yakubu ya kara da cewa hukumar INEC tana da nauyi masu yawa da suka rataya a wuyanta ciki har da gurfanar da masu karya dokar zabe duk da irin kalubalen da hukumar ke fuskanta.

Ya ce tun daga zaben 2015, sun samu laifuka guda 125 game da karya dokar zabe a kotuna mabambanta, amma masu laifi 60 aka iya hukuntawa.

Tun da farko da yake gabatar da kudurin a zauren majalisa, shugaban majalisar wakilai, Hon. Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa rikicin zabe yana janyo karancin inganci da cin hanci da rashawa da rikicin shugabanci, wanda suke taimakawa wajen magudin zabe ta yadda masu laifi suke iya juya gwamnati sabani tsarin dimokuradiyya.

Gbajabiamila wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Hon. Idris Wase ya ce ko shakka babu akwai bukatar yin aiki sosai wajen tsaftace kasar nan daga rikicin zabe da karya dokar zabe.

Kudurin dokar na shafi 19 ya tanadi hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari ga duk wanda aka samu da tsoma baki da taka rawa wajen bayar da rashawa kan zabe.

Sanna sashe na 26 ya tanadi hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari ko tarar naira 40,000, 000 ga duk wanda aka kama da kwacewa ko lalata takardun zabe ko kuma duk wani kundi da ya shafi zabe.

Haka ma sashi na 32 na kudurin dokar ya tanadi hukuncin daurin shekaru 10 ko tarar naira miliyan 40 ga masu kalammun batanci a kan zabe.

Hakazalika, kudurin dokar na shafi 13 ya tanadi hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari ko tarar naira 3,000,000 ga duk wanda aka samu da magudin zabe ko bayar da jawaban karya lokacin da INEC take bayar da katin zabe.

Sannan sashi na 25 ya tanadi hukuncin daurin shekaru biyar ko tarar naira 10,000,000 ga wanda ya lika fostan yakin neman zabe a gida ko a shago ba tare da sanin mai wurin ba, da dai sauran sashi da suka tanadi hukunci ga masu karya dokar zabe.

Idan majalisa ta dawo daga hutu a ranar 20 ga watan Satumbar 2022, za a gudanar da karatu na uku game da wannan kuduri tare da tura kudurin ga majalisar dattawa kafin gabatar wa shugaban kasa domin ya rattaba hannu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
‘Yan Fashi Sun Yi Wa Aubameyang Sata A Gidansa

‘Yan Fashi Sun Yi Wa Aubameyang Sata A Gidansa

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.