ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa Sun Nemi Yanke Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Karya Dokar Zabe

by Yusuf Shuaibu
4 years ago

A kokarin tsaftace harkokin zabe a Nijeriya, ‘yan majalisar wakilai sun gabatar da kuduri na samar da hukunci mai tsanani ga masu karya dokar zabe.

A ranar 23 ga watan Agustan 2023, ‘yan majalisar wakilai sun gudanar da zaman jin ra’ayoyin jama’a, domin samun amincewar masu ruwa da tsaki na neman samar da hukunci mai tsanani ga masu karya dokar zabe.

  • Mace Za Ta Iya Yin Limancin Sallah?
  • Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wani Masallaci Ya Kashe Akalla Mutane 18 A Afganistan

Rikici na daya daga cikin abubuwan da ke damun zaben kasar nan wanda ke tarwatsa lamura gabanin zabe da kuma bayan gudanar da zabe.

ADVERTISEMENT

Dalilan da suke haddasa rikici shi ne bambanci. Irin wadannan laifuka ana amfani da su a wajen abokan takara ko wajen yin mugudi a lokacin zabe.

‘Yan siyasa suna biyan wakilansu wajen yin kalamun batanci ko daukan nauyin ‘yan daba domin farmakar runfar zabe ko sace akwati ko lalata takardun zabe ko sayan kuri’u ko yin garkuwa ko kashe abokan takara da magoya bayansu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Tun kafin babban zaben 2023, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fara fadakarwa.

Amma abun takaicin shi ne, a cikin dokar zaben da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya rattaba hannu a watannin da suka gabata ta kasa samar da tsauraren hukunci da za a yi wa wadanda suka karya dokar zabe.

Domin kawo karshen rikicin zabe, ‘yan majalisa sun samar da kudurin dokar hukunta masu karya dokar zabe wanda ya tsallake karatu na farko da na biyu, inda har ya kai da sauraron jin ra’ayoyin jama’a a kan kudurin.

A wurin zaman jin ra’ayoyin jama’a, Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ya nuna goyon bayansa ga kudurin, wanda ya bayyana cewa lokacin da kudurin ya zama doka, hukumarsa za ta samu kunciyar hankali na tabbatar da an hukunta wadanda suka karya dokar zabe, musamman muyagun ‘yan siyasa masu daukar nauyin ‘yan daba wajen tayar da zaune-tsaye.

A cewarsa, sake fasalin harkokin zabe ba zai yuwu ba har sai an hukunta wadanda suke karya dokar zabe.

Yakubu ya kara da cewa hukumar INEC tana da nauyi masu yawa da suka rataya a wuyanta ciki har da gurfanar da masu karya dokar zabe duk da irin kalubalen da hukumar ke fuskanta.

Ya ce tun daga zaben 2015, sun samu laifuka guda 125 game da karya dokar zabe a kotuna mabambanta, amma masu laifi 60 aka iya hukuntawa.

Tun da farko da yake gabatar da kudurin a zauren majalisa, shugaban majalisar wakilai, Hon. Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa rikicin zabe yana janyo karancin inganci da cin hanci da rashawa da rikicin shugabanci, wanda suke taimakawa wajen magudin zabe ta yadda masu laifi suke iya juya gwamnati sabani tsarin dimokuradiyya.

Gbajabiamila wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Hon. Idris Wase ya ce ko shakka babu akwai bukatar yin aiki sosai wajen tsaftace kasar nan daga rikicin zabe da karya dokar zabe.

Kudurin dokar na shafi 19 ya tanadi hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari ga duk wanda aka samu da tsoma baki da taka rawa wajen bayar da rashawa kan zabe.

Sanna sashe na 26 ya tanadi hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari ko tarar naira 40,000, 000 ga duk wanda aka kama da kwacewa ko lalata takardun zabe ko kuma duk wani kundi da ya shafi zabe.

Haka ma sashi na 32 na kudurin dokar ya tanadi hukuncin daurin shekaru 10 ko tarar naira miliyan 40 ga masu kalammun batanci a kan zabe.

Hakazalika, kudurin dokar na shafi 13 ya tanadi hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari ko tarar naira 3,000,000 ga duk wanda aka samu da magudin zabe ko bayar da jawaban karya lokacin da INEC take bayar da katin zabe.

Sannan sashi na 25 ya tanadi hukuncin daurin shekaru biyar ko tarar naira 10,000,000 ga wanda ya lika fostan yakin neman zabe a gida ko a shago ba tare da sanin mai wurin ba, da dai sauran sashi da suka tanadi hukunci ga masu karya dokar zabe.

Idan majalisa ta dawo daga hutu a ranar 20 ga watan Satumbar 2022, za a gudanar da karatu na uku game da wannan kuduri tare da tura kudurin ga majalisar dattawa kafin gabatar wa shugaban kasa domin ya rattaba hannu.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
‘Yan Fashi Sun Yi Wa Aubameyang Sata A Gidansa

‘Yan Fashi Sun Yi Wa Aubameyang Sata A Gidansa

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.