• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Sabbin Takardun Kudin Da Aka Kaddamar

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Rahotonni, Manyan Labarai
0
‘Yan Nijeriya Na Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Sabbin Takardun Kudin Da Aka Kaddamar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Laraba da ta gabata ce, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da sabbin takardun kudade na Naira 200 da 500 da kuma 1,000, a fadarsa da ke Abuja.

Idan ba a manta ba dai, a ranar 26 ga watan Oktoban 2022 ne, Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (DBN), Godwin Emefiele ya ayyana cewa babban bankin zai sauya fasalin Naira 200 da 500 da kuma 1,000 wanda za su fara aiki a ranar 15 ga watan Disambar 2022, yayin da za a daina amfani da tsofaffin takardun kudade tun daga ranar 31 ga watan Janairun 2023.

  • Gudummawar Kamfanonin Fasahar Sadarwar Kasar Sin Ga Kara Dunkulewar Duniya
  • Zan Magance Rashin Aikin Yin Matasa Da Dala Biliyan 10 – Atiku

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kaddamar da sabbin kudaden, Gwamnan CBN ya shaida wa manema labarai cewa an kaddamar da kudaden ne domin amfanar mutane.

CBN ya ce akwai alfanu sosai game da sauya fasalin takardun Naira wadanda ya kaddamar. Emefiele ya ce daga cikin alfanun da za a samu har da dakile yunkurin buga jabun kudi.

“Alfanun da za a samu na sauya fasalin Naira na da matukar muhimmanci ganin cewa yunkurin zai taimaka wajen rage hauhawar farashi ta hanyar mayar da kudi zuwa bankuna.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

“Sauyin zai tallafa wajen gyara fasalin kudin da kuma samun cikakkun bayanai game da zagayawar kudi a tsakanin jama’a.

“Mun yi imanin cewa hakan zai jawo karuwar jama’a cikin harkokin kudade da kuma rage amfani da sabar kudin.

“Sauya fasalin zai taimaka wajen yaki da rashawa saboda za a kara yawan manyan takardun Naira wadanda su kuma za a iya bin sawunsu daga bankuna cikin sauki,” in ji shi.

Cikin wadanda suka halarci kaddamar da sauya fasalin kudin sun hada da sakata-ren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da shugaban ma’aikatan fadar gwamnati, Farfesa Ibrahim Gambari da shugabar ma’aikatan tarayya, Dakta Folashade Yemi-Esan.

Sauran sun hada da ministodo da gwamnan CBN, Godwin Emefiele.

Sakamakon wannan sauya fasalin takardun kudin, ‘yan Nijeriya da dama sun bayyana ra’ayoyinsu kamar haka:

Shehu Babayo ya bayyana cewa wannan matakin sauya fasalin kudin sanadiyyar arzikin wasu Kenan, sannan kuma sanadiyyar talaucewar wasu Kenan. Allah ya kara mana arziki masu albarka.

Shi kuma Uthman Eedrith ya bayyana cewa yanzu fisabillahi a kan wannan kalar da kuka goga wa kudin shi ne kuka tayar mana da hankali, wanda muka kasa za-ma ko da yaushe muna cikin razana, a she duk a nan za a kare. Wallahi na dauka wata kala mai kyau za a yi da ta sha banban da na da.

Yayin da Auwal Sani Yankaba ya ce A matsayina na dan kasa, ina ba da shawara a sake gyara 1000. Domin bai kamata a rubuta 1000 kawai babu alamar Naira ba, su 500 da 200 ai an saka musu. Yanzu wanda lambobi kawai ya iya karantawa ta ya ya zai gane Naira ce ko Sefa ce, ko kuma dala ce?

A cewar Abubakar Moh’d Idris, haba su kuwa, me ya sa ba za a dan sauya fasalin irin rubutun da ke jikin kudaden ba. Ya kamata da an dan kara wasu ‘yan abubuwa daya ko biyu a jikin kowanne takardan kudin. Kawai an canza fenti bayan komai yana nan kamar yadda yake. Kenan sai mutane su rina nasu su dunga bai wa mu-tane da daddare.

Auwal Abdurrahman Idris ya de Allah sarki kasata, abin da take so a yi mata ba shi ake yi ba. Ya mamallakin mutum da Aljan mai juya komai a karkashin mulkinsa muna dada tuba a gareka, ya Malikal mulki tutal mulka ka dube mu da rahamarka da jin kanka ga bayinka dikin matsi da kundin rayuwa ka yafe mana zunubanmu, ba dan halinmuba, sannan ka shirye mu zuwa biyayya agare ka, ka ceto mu, san-nan ka ceci kasarmu daga hannun azzaluman shugabanin kasarmu ta Nijeriya, domin mutundin Muhammadu Rasulullahi (S A W).

Wannan shi ne irin martani da wasu ‘yan Nijeriya suka bayyana a kan saurya fa-salin kudade da gwamnatin tarayya da kaddamar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKaddamarwaNairaSabbin Kudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Fitaccen Mawakin ‘Bauchi Sai Bala’ Ya Fice Daga Tafiyar Bala Ya Koma Mara Wa Sadiqu Na APC Baya

Next Post

Ambaliyar Ruwa: Ministar Jinkai Ta Kaddamar Da Rabon Tallafi Ga Mutum 5,428 A Neja

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

6 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

8 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

14 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

15 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

18 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

1 day ago
Next Post
Ambaliyar Ruwa: Ministar Jinkai Ta Kaddamar Da Rabon Tallafi Ga Mutum 5,428 A Neja

Ambaliyar Ruwa: Ministar Jinkai Ta Kaddamar Da Rabon Tallafi Ga Mutum 5,428 A Neja

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.