• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Koka Da Kara Kudin Litar Mai

by Khalid Idris Doya
9 months ago
Mai

Matatar man Dangote da kungiyar dillalan Man Fetur a Nijeriya sun daura alhalin tashin farashin mai na baya-bayan nan da karuwar farashin danyen mai a kasuwar duniya, yayin da ‘yan Nijeriya suka koka da wannan karin.

‘Yan Nijeriya dai sun wayi garin ranar Juma’a da sabon karin kudin man fetur a fadin kasar nan, inda suka nuna hakan a matsayin koma-baya.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Yajin Aikin Likitoci Ya Tsayar Da Al’amura A Asibitocin Abuja

Matatar mai ta Dangote ta kara farashin manta daga naira 899.50 kan kowace lita zuwa naira 950, inda ke nuni da an samu karin naira 50 wato kaso 5.

Bayan hakan, gidajen mai kuma sun kara farashin da suke sayar da litar mai kama daga naira 970 da naira 1,150 daga naira 935 zuwa naira 1,100 a kan kowace lita.

A wata sanarwar da kakakin matatar mai ta Dangote, Anthony Chijiena, ya fitar, ya yi bayanin cewa an samu karin farashin danyen mai a duniyance daga dala 70 zuwa dala 82 kan kowace ganga.

LABARAI MASU NASABA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Ya ce, “Matatar Dangote ta dauki kusan kashi 50 cikin 100 na farashin da ake samu a kasuwannin mai na duniya. Wannan ya faru ne saboda jajircewar da muka yi na samar da man da inganci da arha, da kuma mallakar matatar man da ‘yan Nijeriya ke yi, wanda ya kasance jigon ayyukanmu. Idan matatar Dangote za ta kai duk wani karin farashin danyen mai zuwa kasuwa, farashin dillalan man zai kai kusan naira 1,150 zuwa naira 1,200 kowace lita a wasu wurare, idan aka kwatanta da farashin na naira 970 a halin yanzu.”

Su ma a bangarensu, PETROAN, ta cikin sanarwar da kakakinta, Joseph Obele, ya fitar, shi ma ya daura alhalin karin da tashin farashin danyen mai a kasuwar duniya.

Da yake nakalto abun da shugaban kungiyar PETROAN, Billy Gillis-Harry, ke cewa, tabbas tashin farashin dayen mai a kasuwar duniya zai shafi tace mai a Nijeriya.

“Tabbas tashin da saukar farashin mai na shafan gidajen manmu. Kuma yana shafan kasuwancinmu ma.

“Ko da yaushe farashin da muka sayar da kayanmu na samu asali ne daga yadda muka saya. Don haka, ka da a zargi mambobinmu da karin kudin mai da ake fuskanta a halin yanzu,” ya shaida.

Sai dai kuma ‘yan Nijeriya da dama sun nuna matukar damuwarsu kan wannan lamarin. Farfesa Theophilus Ndubuaku, ya ce, sabon karin kudin mai tunin ya shafi farashin kayan abinci da kudin sufuri.

Suleiman Abubakar, mazaunin Abuja, ya ce kwanakin da ke gaba za su zama masu wuya ga al’ummar kasa sakamakon wannan karin kudin Lltar mai da aka samu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Next Post
Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina – UNICEF

Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina - UNICEF

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.