ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Koka Da Kara Kudin Litar Mai

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Mai

Matatar man Dangote da kungiyar dillalan Man Fetur a Nijeriya sun daura alhalin tashin farashin mai na baya-bayan nan da karuwar farashin danyen mai a kasuwar duniya, yayin da ‘yan Nijeriya suka koka da wannan karin.

‘Yan Nijeriya dai sun wayi garin ranar Juma’a da sabon karin kudin man fetur a fadin kasar nan, inda suka nuna hakan a matsayin koma-baya.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Yajin Aikin Likitoci Ya Tsayar Da Al’amura A Asibitocin Abuja

Matatar mai ta Dangote ta kara farashin manta daga naira 899.50 kan kowace lita zuwa naira 950, inda ke nuni da an samu karin naira 50 wato kaso 5.

ADVERTISEMENT

Bayan hakan, gidajen mai kuma sun kara farashin da suke sayar da litar mai kama daga naira 970 da naira 1,150 daga naira 935 zuwa naira 1,100 a kan kowace lita.

A wata sanarwar da kakakin matatar mai ta Dangote, Anthony Chijiena, ya fitar, ya yi bayanin cewa an samu karin farashin danyen mai a duniyance daga dala 70 zuwa dala 82 kan kowace ganga.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Ya ce, “Matatar Dangote ta dauki kusan kashi 50 cikin 100 na farashin da ake samu a kasuwannin mai na duniya. Wannan ya faru ne saboda jajircewar da muka yi na samar da man da inganci da arha, da kuma mallakar matatar man da ‘yan Nijeriya ke yi, wanda ya kasance jigon ayyukanmu. Idan matatar Dangote za ta kai duk wani karin farashin danyen mai zuwa kasuwa, farashin dillalan man zai kai kusan naira 1,150 zuwa naira 1,200 kowace lita a wasu wurare, idan aka kwatanta da farashin na naira 970 a halin yanzu.”

Su ma a bangarensu, PETROAN, ta cikin sanarwar da kakakinta, Joseph Obele, ya fitar, shi ma ya daura alhalin karin da tashin farashin danyen mai a kasuwar duniya.

Da yake nakalto abun da shugaban kungiyar PETROAN, Billy Gillis-Harry, ke cewa, tabbas tashin farashin dayen mai a kasuwar duniya zai shafi tace mai a Nijeriya.

“Tabbas tashin da saukar farashin mai na shafan gidajen manmu. Kuma yana shafan kasuwancinmu ma.

“Ko da yaushe farashin da muka sayar da kayanmu na samu asali ne daga yadda muka saya. Don haka, ka da a zargi mambobinmu da karin kudin mai da ake fuskanta a halin yanzu,” ya shaida.

Sai dai kuma ‘yan Nijeriya da dama sun nuna matukar damuwarsu kan wannan lamarin. Farfesa Theophilus Ndubuaku, ya ce, sabon karin kudin mai tunin ya shafi farashin kayan abinci da kudin sufuri.

Suleiman Abubakar, mazaunin Abuja, ya ce kwanakin da ke gaba za su zama masu wuya ga al’ummar kasa sakamakon wannan karin kudin Lltar mai da aka samu.

Mai
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina – UNICEF

Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina - UNICEF

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.