ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Koka Da Kara Kudin Litar Mai

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Mai

Matatar man Dangote da kungiyar dillalan Man Fetur a Nijeriya sun daura alhalin tashin farashin mai na baya-bayan nan da karuwar farashin danyen mai a kasuwar duniya, yayin da ‘yan Nijeriya suka koka da wannan karin.

‘Yan Nijeriya dai sun wayi garin ranar Juma’a da sabon karin kudin man fetur a fadin kasar nan, inda suka nuna hakan a matsayin koma-baya.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Yajin Aikin Likitoci Ya Tsayar Da Al’amura A Asibitocin Abuja

Matatar mai ta Dangote ta kara farashin manta daga naira 899.50 kan kowace lita zuwa naira 950, inda ke nuni da an samu karin naira 50 wato kaso 5.

ADVERTISEMENT

Bayan hakan, gidajen mai kuma sun kara farashin da suke sayar da litar mai kama daga naira 970 da naira 1,150 daga naira 935 zuwa naira 1,100 a kan kowace lita.

A wata sanarwar da kakakin matatar mai ta Dangote, Anthony Chijiena, ya fitar, ya yi bayanin cewa an samu karin farashin danyen mai a duniyance daga dala 70 zuwa dala 82 kan kowace ganga.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Ya ce, “Matatar Dangote ta dauki kusan kashi 50 cikin 100 na farashin da ake samu a kasuwannin mai na duniya. Wannan ya faru ne saboda jajircewar da muka yi na samar da man da inganci da arha, da kuma mallakar matatar man da ‘yan Nijeriya ke yi, wanda ya kasance jigon ayyukanmu. Idan matatar Dangote za ta kai duk wani karin farashin danyen mai zuwa kasuwa, farashin dillalan man zai kai kusan naira 1,150 zuwa naira 1,200 kowace lita a wasu wurare, idan aka kwatanta da farashin na naira 970 a halin yanzu.”

Su ma a bangarensu, PETROAN, ta cikin sanarwar da kakakinta, Joseph Obele, ya fitar, shi ma ya daura alhalin karin da tashin farashin danyen mai a kasuwar duniya.

Da yake nakalto abun da shugaban kungiyar PETROAN, Billy Gillis-Harry, ke cewa, tabbas tashin farashin dayen mai a kasuwar duniya zai shafi tace mai a Nijeriya.

“Tabbas tashin da saukar farashin mai na shafan gidajen manmu. Kuma yana shafan kasuwancinmu ma.

“Ko da yaushe farashin da muka sayar da kayanmu na samu asali ne daga yadda muka saya. Don haka, ka da a zargi mambobinmu da karin kudin mai da ake fuskanta a halin yanzu,” ya shaida.

Sai dai kuma ‘yan Nijeriya da dama sun nuna matukar damuwarsu kan wannan lamarin. Farfesa Theophilus Ndubuaku, ya ce, sabon karin kudin mai tunin ya shafi farashin kayan abinci da kudin sufuri.

Suleiman Abubakar, mazaunin Abuja, ya ce kwanakin da ke gaba za su zama masu wuya ga al’ummar kasa sakamakon wannan karin kudin Lltar mai da aka samu.

Mai
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina – UNICEF

Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina - UNICEF

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.