ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Uwan Marigayiya Nabeeha Su 5 Da Ɓarayin Mutane Suka Sace Sun Shaƙi Iskar ‘Yanci

by Muhammad
2 years ago
Nabeeha

Jami’an tsaro sun ceto wasu ’yan mata biyar ‘yan uwan Marigayiya Nabeeha da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a unguwar Bwari da ke Abuja. 

LEADERSHIP ta rawaito cewa an yi garkuwa da wasu ‘yan uwan juna ‘yan gida daya su shida a Unguwar Bwari da ke Abuja a ranar 2 ga watan Janairu 2024.

  • ‘Yan Bindiga Sun Harbe Dan Shekara 7 Bayan Garkuwa Da Mutum 10 A Abuja
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9

Masu garkuwa da mutane sun kashe daya daga cikin mai suna Nabeeha a makon jiya. Bayan kashe wani dalibi da ke karatun digiri, an ce barayin sun bukaci fansar kudi daga Naira miliyan 60 zuwa Naira miliyan 100, yayin da suna masu barazanar kashe sauran ‘yan uwa matan da ke hannunsu.

ADVERTISEMENT

A ranar Lahadin da ta gabata ne tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Nijeriya, Farfesa Isa Pantami, ya sanar da bukatar neman tara Naira miliyan 50 ga iyalan wadanda aka yi garkuwa da su don jama’a su taimaka a biya kudin fansar ‘yan matan don ganin an sako sauran ‘yan matan. .

Daya daga cikin ‘yan uwan Najeeba da suka kubuta, ta bayyana irin halin da suka shiga a cikin sakonta da ta wallafa a shafin X (Twitter) don nuna godiya ga ‘yan Nijeriya biyo bayan ceto su da jami’an tsaro suka yi.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

“Ina matukar godiya da addu’o’inku da goyon bayanku a tsawon wannan lokacin jarabawar. Wannan shi ne mafi girman jarabawar a rayuwata wallahi amma da yake rahmar Allah na da fadi, ga shi komai ya zo karshe, Na gode muku gabadaya.” Cewarta.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Abuja, Josephine Adeh, ta ce ‘yan uwa mata tare da wasu da aka yi garkuwa da su a yankin Bwari, jami’an tsaron sun ceto su ne daga dajin Kajuru na jihar Kaduna.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa an ceto ‘yan uwa ‘yan matan da wasu da aka yi garkuwa da su a wani dajin da ke makwabtaka da jihar Kaduna tare da hadin guiwar jami’an tsaro.

“Jami’an sun yi nasarar ceto wadanda abin ya shafa a dajin Kajuru a jihar Kaduna da misalin karfe 11:30 na daren ranar Asabar 20 ga watan Janairu, 2024,” cewar Kakakin rundunar ‘yan sandan Abuja, Josephine Adeh.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN
Labarai

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Next Post
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha

Wani Jariri Ya Ɓata A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.