• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai abubuwan da suka ja hankali a lokacin yanke hukunci a kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa, wanda ya gudana a Abuja a wannan makon da muke ciki.

 Kotun sauraron kararrakin zaben na shugaban kasa, ta yi watsi da galibin korafe-korafen da aka shigar a karar da Mista Peter Obi na jam’iyyar LP da Atiku Abubakar na PDP suka shigar a kan kalubalantar nasarar Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun 2023.

  • Zabe: Obi Ya Gaza Bayyana Yadda Ya Samu Kuri’u Masu Rinjaye – Kotun Zaben Shugaban Ƙasa
  • Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Mai shari’a Haruna Tsammani, wanda ya jagoranci kwamitin Alkalan guda 5 na kotun sauraren kararrakin zaben shugaban kasa ya yi watsi da karar sakamakon rashin nagarta, inda ya kara da cewa masu shigar da kara sun kasa tabbatar da zargin da suka yi kan zaben.

Obi da jam’iyyarsa a cikin karar da suka shigar a watan Maris na wannan shekara, sun yi ikirarin cewa Tinubu bai samu rinjayen kuri’un da aka kada a zaben shugaban kasar da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu ba.

Bugu da kari, sun yi zargin cewa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ba ta bi ka’idar da doka ta shimfida ba wajen ayyana Tinubun a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Bayan haka, Obi da LP sun yi ikirarin cewa bai kamata Tinubu ya kasance a zaben ba, saboda hanyar da ya bi wajen zaben mataimakinsa ba bisa ka’ida ba da kuma zarge-zargen da wata kotu a Amurka ta yi masa a shekarar 1990.

Masu shigar da karar, sun zargi INEC da ayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben da bai samu kashi 25 na kuri’un da aka kada a Babban Birnin Tarayya (Abuja) ba.

Sai dai da yake yanke hukunci a cikin karar ranar Larabar da ta gabata, Mai Shari’a Tsammani ya ce wadanda suka shigar da karar sun kasa tabbatar da zarge-zargen da suke yi na tafka magudi, rashin bin ka’ida da kuma ayyukan rashawa da aka yi a zaben.

A kan batun rashin samun kashi 25 da Tinubu ya gaza samu a cikin Babban Birnin Tarayya, kotun ta ce Abuja daidai take da kowace jiha a Nijeriya.

Kotun ta yi nuni da cewa, kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya bayyana cewa dukkanin ‘yan kasa daidai suke, babu wanda ya fi wani ko kasa da wani ta hanyar zabe.

Tsammani ya yi nuni da cewa, masu shigar da kara sun yi fassarar sashe na 134 na kundin tsarin mulkin kasar, ba daidai ba, inda suka dauka cewa masu kada kuri’a na Abuja sun fi kima ga wasu jihohi.

Kotun ta ce sashe na 299 na kundin tsarin mulkin kasar, ya ce, “ Abuja kamar kowace jiha take” kuma ba ta fi sauran jihohi ba.

Tsammani ya kara da cewa, “Bayan an warware dukkanin batutuwan guda uku don goyon bayan wadanda ake kara, shari’ar wadanda suka shigar da kara ta kasance mara tushe da kuma nagarta.”

Sai dai kuma jam’iyyar LP ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasar da ta tabbatar da Bola Tinubu na jam’iyyar APC, a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 25 ga Fabrairun, 2023.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Obiora Ifoh, ya bayyana matsayin jam’iyyar a Abuja, jim kadan bayan kotun ta bayyana hukuncin nata.

Ifoh ya ce, “Jam’iyyar LP ta yi watsi da karar da kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa, karkashin jagorancin mai shari’a Haruna Tsammani ta yi a yau, kuma ba za mu amince da sakamakon hukuncin da aka yanke ba, saboda ba a yi adalci ko kadan ba.

“’Yan Nijeriya shaidu ne kan zaben da aka yi a ranar 25 ga Fabrairun 2023, wanda duniya ta yi Allah wadai da shi amma kotun ta yi watsi da hujjojinmu.”

“Demokuradiyya ake yi kuma ba za mu yi kasa a guiwa ba, har sai mun kai ga yin nasara. Kazalika, muna jinjina wa tawagar kungiyar lauyoyinmu da suka yi namijin kokari a kan wannan shari’a.

Muna ikirarin mulkin dimokuradiyya a Nijeriya ne kawai, amma ba ita ake yi ba, domin haka ba za mu yi kasa a guiwa ba,

Za mu gabatar da cikakkun bayanai game da matsayar jam’iyyarmu, bayan tattaunawa da lauyoyinmu domin cimma matsaya,” in ji shi .

“Haka nan, muna kira ga dukkanin masoya mulkin dimokuradiyya da su mai da hankali da kwarin guiwa domin kawo sauyi a Nijeriya.”

Har ila yau, kotun sauraron karar zaben shugaban kasar ta kori zargin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar kan cewa, Tinubu ba dan kasa ba ne sannan kuma yana ta’ammali da miyagun kwayoyi.

Yayin da kotun ta yi watsi da karar Atiku kan zargin cewa Tinubu yana amfani da takardar kasashe guda biyu. Haka kuma ta yi fatali da zargi cewa Tinubu bai cancanci ya tsaya takarar shugabancin Nijeriya ba.

Haka kuma, an hango wasu daga cikin mahalarta kotun sauraron karar zaben shugaban kasar, na ta faman sharbar bacci kafin yanke hukuncin.

Haka nan wani lauya ya yi kokarin gabatar da korafi, sai dai Alkalan kotun sun ki ki amincewa tare da ankarar da shi cewa ya bari idan yana da magana bayan yanke hukunci sai ya yi nazari ya san matakin da zai dauka.

Wannan hukunci ko kadan bai yi wa bangaren Obi da Atiku dadi ba, inda ake ganin cewa ko shakka babu za su garzaya zuwa Kotun Koli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwana 100 Na Mulkin Tinubu; Da Gaske Bayan Duhu Sai Haske?

Next Post

Takaddamar Zaben Gwamnan Jihar Kaduna…

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Takaddamar Zaben Gwamnan Jihar Kaduna…

Takaddamar Zaben Gwamnan Jihar Kaduna…

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.