ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Zaben

Akwai abubuwan da suka ja hankali a lokacin yanke hukunci a kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa, wanda ya gudana a Abuja a wannan makon da muke ciki.

 Kotun sauraron kararrakin zaben na shugaban kasa, ta yi watsi da galibin korafe-korafen da aka shigar a karar da Mista Peter Obi na jam’iyyar LP da Atiku Abubakar na PDP suka shigar a kan kalubalantar nasarar Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun 2023.

  • Zabe: Obi Ya Gaza Bayyana Yadda Ya Samu Kuri’u Masu Rinjaye – Kotun Zaben Shugaban Ƙasa
  • Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Mai shari’a Haruna Tsammani, wanda ya jagoranci kwamitin Alkalan guda 5 na kotun sauraren kararrakin zaben shugaban kasa ya yi watsi da karar sakamakon rashin nagarta, inda ya kara da cewa masu shigar da kara sun kasa tabbatar da zargin da suka yi kan zaben.

ADVERTISEMENT

Obi da jam’iyyarsa a cikin karar da suka shigar a watan Maris na wannan shekara, sun yi ikirarin cewa Tinubu bai samu rinjayen kuri’un da aka kada a zaben shugaban kasar da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu ba.

Bugu da kari, sun yi zargin cewa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ba ta bi ka’idar da doka ta shimfida ba wajen ayyana Tinubun a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Bayan haka, Obi da LP sun yi ikirarin cewa bai kamata Tinubu ya kasance a zaben ba, saboda hanyar da ya bi wajen zaben mataimakinsa ba bisa ka’ida ba da kuma zarge-zargen da wata kotu a Amurka ta yi masa a shekarar 1990.

Masu shigar da karar, sun zargi INEC da ayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben da bai samu kashi 25 na kuri’un da aka kada a Babban Birnin Tarayya (Abuja) ba.

Sai dai da yake yanke hukunci a cikin karar ranar Larabar da ta gabata, Mai Shari’a Tsammani ya ce wadanda suka shigar da karar sun kasa tabbatar da zarge-zargen da suke yi na tafka magudi, rashin bin ka’ida da kuma ayyukan rashawa da aka yi a zaben.

A kan batun rashin samun kashi 25 da Tinubu ya gaza samu a cikin Babban Birnin Tarayya, kotun ta ce Abuja daidai take da kowace jiha a Nijeriya.

Kotun ta yi nuni da cewa, kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya bayyana cewa dukkanin ‘yan kasa daidai suke, babu wanda ya fi wani ko kasa da wani ta hanyar zabe.

Tsammani ya yi nuni da cewa, masu shigar da kara sun yi fassarar sashe na 134 na kundin tsarin mulkin kasar, ba daidai ba, inda suka dauka cewa masu kada kuri’a na Abuja sun fi kima ga wasu jihohi.

Kotun ta ce sashe na 299 na kundin tsarin mulkin kasar, ya ce, “ Abuja kamar kowace jiha take” kuma ba ta fi sauran jihohi ba.

Tsammani ya kara da cewa, “Bayan an warware dukkanin batutuwan guda uku don goyon bayan wadanda ake kara, shari’ar wadanda suka shigar da kara ta kasance mara tushe da kuma nagarta.”

Sai dai kuma jam’iyyar LP ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasar da ta tabbatar da Bola Tinubu na jam’iyyar APC, a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 25 ga Fabrairun, 2023.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Obiora Ifoh, ya bayyana matsayin jam’iyyar a Abuja, jim kadan bayan kotun ta bayyana hukuncin nata.

Ifoh ya ce, “Jam’iyyar LP ta yi watsi da karar da kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa, karkashin jagorancin mai shari’a Haruna Tsammani ta yi a yau, kuma ba za mu amince da sakamakon hukuncin da aka yanke ba, saboda ba a yi adalci ko kadan ba.

“’Yan Nijeriya shaidu ne kan zaben da aka yi a ranar 25 ga Fabrairun 2023, wanda duniya ta yi Allah wadai da shi amma kotun ta yi watsi da hujjojinmu.”

“Demokuradiyya ake yi kuma ba za mu yi kasa a guiwa ba, har sai mun kai ga yin nasara. Kazalika, muna jinjina wa tawagar kungiyar lauyoyinmu da suka yi namijin kokari a kan wannan shari’a.

Muna ikirarin mulkin dimokuradiyya a Nijeriya ne kawai, amma ba ita ake yi ba, domin haka ba za mu yi kasa a guiwa ba,

Za mu gabatar da cikakkun bayanai game da matsayar jam’iyyarmu, bayan tattaunawa da lauyoyinmu domin cimma matsaya,” in ji shi .

“Haka nan, muna kira ga dukkanin masoya mulkin dimokuradiyya da su mai da hankali da kwarin guiwa domin kawo sauyi a Nijeriya.”

Har ila yau, kotun sauraron karar zaben shugaban kasar ta kori zargin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar kan cewa, Tinubu ba dan kasa ba ne sannan kuma yana ta’ammali da miyagun kwayoyi.

Yayin da kotun ta yi watsi da karar Atiku kan zargin cewa Tinubu yana amfani da takardar kasashe guda biyu. Haka kuma ta yi fatali da zargi cewa Tinubu bai cancanci ya tsaya takarar shugabancin Nijeriya ba.

Haka kuma, an hango wasu daga cikin mahalarta kotun sauraron karar zaben shugaban kasar, na ta faman sharbar bacci kafin yanke hukuncin.

Haka nan wani lauya ya yi kokarin gabatar da korafi, sai dai Alkalan kotun sun ki ki amincewa tare da ankarar da shi cewa ya bari idan yana da magana bayan yanke hukunci sai ya yi nazari ya san matakin da zai dauka.

Wannan hukunci ko kadan bai yi wa bangaren Obi da Atiku dadi ba, inda ake ganin cewa ko shakka babu za su garzaya zuwa Kotun Koli.

Zaben
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Takaddamar Zaben Gwamnan Jihar Kaduna…

Takaddamar Zaben Gwamnan Jihar Kaduna…

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.