• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Dalibai 3, Da Wani Bisa Zargin Shiga Kungiyar Asiri A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
'Yansanda

Hedikwatar rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta sanar da cewa, ta cafke wasu dalibai guda uku da wani mutum daya bisa zarginsu da kasance cikin kungiyar asiri mai suna Black axe.

Wadanda aka kama bisa wannan zargin, su ne, Eric Nuhu mai shekara 23 – dalibi ne da ke matakin karshe a jami’ar ATBU da ke Bauchi; Zaharaddeen Hassan, dan shekara 19, da ke matakin karatu (ND 1) a kwalejin kimiyya da fasaha ta gwamnatin tarayya da ke Bauchi; Felix John dan shekara 24 – dalibin karatu da ke (HND 1) a kwalejin kimiyya da fasaha mallakin gwamnatin tarayya da ke Bauchi; da kuma wani mai suna Daniel Masaka dan karamar hukumar Karu a jihar Nasarawa.

  • Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa

A sanarwar manema labarai da kakakin ‘yansandan jihar Bauchi, SP Ahmed Muhammad Wakil ya fitar a ranar Juma’a, ya ce, a bisa binciken da suka yi, sun gano cewa, mutum biyu daga cikin wadanda ake zargin na farko da na biyu sun bayyana cewa, wani abokin karatunsu ne, Abbas Apeh da ke matakin karshe a jami’ar ATBU Bauchi ne ya gayyace su shiga cikin kungiyar a ranar 2 ga watan Satumban 2023.

Sauran kuma da ake zargin, sun tabbatar da cewa sun jima da kasancewa mambobin kungiyar asirin ta Black axe.

Ya ce, mambobin kungiyar ne suka gayyacesu domin su halarci wani bikin tarbar amsar sabbin mambobi da aka gudanar a wani waje a Bauchi da ke kusa da matsugunin jami’ar ATBU na dindindin da ke Gubi a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Kano.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Kazalika, a wani labarin makamancin wannan, rundunar ta kuma kama wasu mutum biyu da suka kasance kwararru a bangaren kwacen mashina kuma sun shafe sama da shekaru hudu suna tsula tsiyarsu a cikin kwaryar Bauchi da jihohin makwafta.

A ranar 24 ga watan Agustan, wani mutum mai suna one Aliyu Muhammad Gidado mazaunin unguwar tsohowar Airport inda ya kai rahoto ga ‘yansanda cewa a wannan ranar ya gano wani Bello Mohammed da aka fi sani da Faruk Manja dan shekara 30 mazaunin unguwar Bakaro shi da wani mai suna Kabiru Danfulani da ke Muda Lawal Bauchi (da yanzu ake nema) sun shiga cikin gidansa tare da sace masa mota kirar Honda Civic mai lamba MSA-350-PD da kudinta ya kai naira N640,000;00 tare da wata kwarangwal din mashin hadi da wasu kadarorin da ba a tantance adadinsu ba zuwa yanzu.

Wakil ya ce bayan da suka kaddamar da bincike sun kamo wanda ake zargi da kuma abubuwan da suka sace a lokacin da suke kokarin arcewa.

A cewarsa a lokacin bincike wanda ake zargi na farko ya ce, ya shafe shekaru hudu yana satar mashina kuma zuwa yanzu ya sace mashina za su kai 20 a jihohin Bauchi da Yobe. yayin da shi kuma wanda ake zargi na biyun ya gudu.

Sanarwar ta ce za su gudanar da wadanda suke zargin a gaban kotu da zarar suka kammala gudanar da bincike.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abduljabbar
Labarai

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Next Post
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

...Ya Kashe Uwargidan Da Yake Yi Wa Hidima Da Mahaifiyarta Gami Da Tafka Sata

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.