• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Dalibai 3, Da Wani Bisa Zargin Shiga Kungiyar Asiri A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Cafke Dalibai 3, Da Wani Bisa Zargin Shiga Kungiyar Asiri A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hedikwatar rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta sanar da cewa, ta cafke wasu dalibai guda uku da wani mutum daya bisa zarginsu da kasance cikin kungiyar asiri mai suna Black axe.

Wadanda aka kama bisa wannan zargin, su ne, Eric Nuhu mai shekara 23 – dalibi ne da ke matakin karshe a jami’ar ATBU da ke Bauchi; Zaharaddeen Hassan, dan shekara 19, da ke matakin karatu (ND 1) a kwalejin kimiyya da fasaha ta gwamnatin tarayya da ke Bauchi; Felix John dan shekara 24 – dalibin karatu da ke (HND 1) a kwalejin kimiyya da fasaha mallakin gwamnatin tarayya da ke Bauchi; da kuma wani mai suna Daniel Masaka dan karamar hukumar Karu a jihar Nasarawa.

  • Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa

A sanarwar manema labarai da kakakin ‘yansandan jihar Bauchi, SP Ahmed Muhammad Wakil ya fitar a ranar Juma’a, ya ce, a bisa binciken da suka yi, sun gano cewa, mutum biyu daga cikin wadanda ake zargin na farko da na biyu sun bayyana cewa, wani abokin karatunsu ne, Abbas Apeh da ke matakin karshe a jami’ar ATBU Bauchi ne ya gayyace su shiga cikin kungiyar a ranar 2 ga watan Satumban 2023.

Sauran kuma da ake zargin, sun tabbatar da cewa sun jima da kasancewa mambobin kungiyar asirin ta Black axe.

Ya ce, mambobin kungiyar ne suka gayyacesu domin su halarci wani bikin tarbar amsar sabbin mambobi da aka gudanar a wani waje a Bauchi da ke kusa da matsugunin jami’ar ATBU na dindindin da ke Gubi a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Kano.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Kazalika, a wani labarin makamancin wannan, rundunar ta kuma kama wasu mutum biyu da suka kasance kwararru a bangaren kwacen mashina kuma sun shafe sama da shekaru hudu suna tsula tsiyarsu a cikin kwaryar Bauchi da jihohin makwafta.

A ranar 24 ga watan Agustan, wani mutum mai suna one Aliyu Muhammad Gidado mazaunin unguwar tsohowar Airport inda ya kai rahoto ga ‘yansanda cewa a wannan ranar ya gano wani Bello Mohammed da aka fi sani da Faruk Manja dan shekara 30 mazaunin unguwar Bakaro shi da wani mai suna Kabiru Danfulani da ke Muda Lawal Bauchi (da yanzu ake nema) sun shiga cikin gidansa tare da sace masa mota kirar Honda Civic mai lamba MSA-350-PD da kudinta ya kai naira N640,000;00 tare da wata kwarangwal din mashin hadi da wasu kadarorin da ba a tantance adadinsu ba zuwa yanzu.

Wakil ya ce bayan da suka kaddamar da bincike sun kamo wanda ake zargi da kuma abubuwan da suka sace a lokacin da suke kokarin arcewa.

A cewarsa a lokacin bincike wanda ake zargi na farko ya ce, ya shafe shekaru hudu yana satar mashina kuma zuwa yanzu ya sace mashina za su kai 20 a jihohin Bauchi da Yobe. yayin da shi kuma wanda ake zargi na biyun ya gudu.

Sanarwar ta ce za su gudanar da wadanda suke zargin a gaban kotu da zarar suka kammala gudanar da bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Taya Malaman Kasar Sin Murnar Ranarsu

Next Post

…Ya Kashe Uwargidan Da Yake Yi Wa Hidima Da Mahaifiyarta Gami Da Tafka Sata

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

22 minutes ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

2 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

3 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

4 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

7 hours ago
Next Post
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

...Ya Kashe Uwargidan Da Yake Yi Wa Hidima Da Mahaifiyarta Gami Da Tafka Sata

LABARAI MASU NASABA

Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.