• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Dalibai 3, Da Wani Bisa Zargin Shiga Kungiyar Asiri A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Cafke Dalibai 3, Da Wani Bisa Zargin Shiga Kungiyar Asiri A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hedikwatar rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta sanar da cewa, ta cafke wasu dalibai guda uku da wani mutum daya bisa zarginsu da kasance cikin kungiyar asiri mai suna Black axe.

Wadanda aka kama bisa wannan zargin, su ne, Eric Nuhu mai shekara 23 – dalibi ne da ke matakin karshe a jami’ar ATBU da ke Bauchi; Zaharaddeen Hassan, dan shekara 19, da ke matakin karatu (ND 1) a kwalejin kimiyya da fasaha ta gwamnatin tarayya da ke Bauchi; Felix John dan shekara 24 – dalibin karatu da ke (HND 1) a kwalejin kimiyya da fasaha mallakin gwamnatin tarayya da ke Bauchi; da kuma wani mai suna Daniel Masaka dan karamar hukumar Karu a jihar Nasarawa.

  • Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa

A sanarwar manema labarai da kakakin ‘yansandan jihar Bauchi, SP Ahmed Muhammad Wakil ya fitar a ranar Juma’a, ya ce, a bisa binciken da suka yi, sun gano cewa, mutum biyu daga cikin wadanda ake zargin na farko da na biyu sun bayyana cewa, wani abokin karatunsu ne, Abbas Apeh da ke matakin karshe a jami’ar ATBU Bauchi ne ya gayyace su shiga cikin kungiyar a ranar 2 ga watan Satumban 2023.

Sauran kuma da ake zargin, sun tabbatar da cewa sun jima da kasancewa mambobin kungiyar asirin ta Black axe.

Ya ce, mambobin kungiyar ne suka gayyacesu domin su halarci wani bikin tarbar amsar sabbin mambobi da aka gudanar a wani waje a Bauchi da ke kusa da matsugunin jami’ar ATBU na dindindin da ke Gubi a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Kano.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

Kazalika, a wani labarin makamancin wannan, rundunar ta kuma kama wasu mutum biyu da suka kasance kwararru a bangaren kwacen mashina kuma sun shafe sama da shekaru hudu suna tsula tsiyarsu a cikin kwaryar Bauchi da jihohin makwafta.

A ranar 24 ga watan Agustan, wani mutum mai suna one Aliyu Muhammad Gidado mazaunin unguwar tsohowar Airport inda ya kai rahoto ga ‘yansanda cewa a wannan ranar ya gano wani Bello Mohammed da aka fi sani da Faruk Manja dan shekara 30 mazaunin unguwar Bakaro shi da wani mai suna Kabiru Danfulani da ke Muda Lawal Bauchi (da yanzu ake nema) sun shiga cikin gidansa tare da sace masa mota kirar Honda Civic mai lamba MSA-350-PD da kudinta ya kai naira N640,000;00 tare da wata kwarangwal din mashin hadi da wasu kadarorin da ba a tantance adadinsu ba zuwa yanzu.

Wakil ya ce bayan da suka kaddamar da bincike sun kamo wanda ake zargi da kuma abubuwan da suka sace a lokacin da suke kokarin arcewa.

A cewarsa a lokacin bincike wanda ake zargi na farko ya ce, ya shafe shekaru hudu yana satar mashina kuma zuwa yanzu ya sace mashina za su kai 20 a jihohin Bauchi da Yobe. yayin da shi kuma wanda ake zargi na biyun ya gudu.

Sanarwar ta ce za su gudanar da wadanda suke zargin a gaban kotu da zarar suka kammala gudanar da bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Taya Malaman Kasar Sin Murnar Ranarsu

Next Post

…Ya Kashe Uwargidan Da Yake Yi Wa Hidima Da Mahaifiyarta Gami Da Tafka Sata

Related

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

1 hour ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

10 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

11 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

12 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

13 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

15 hours ago
Next Post
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

...Ya Kashe Uwargidan Da Yake Yi Wa Hidima Da Mahaifiyarta Gami Da Tafka Sata

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.