• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

by Muhammad
4 hours ago
in Labarai, Siyasa
0
‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘Yansanda a Jihar Kaduna ta hana gudanar da taron da magoya bayan ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, suka shirya don bikin zagayowar ranar haihuwarsa a jihar.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar, ‘yansandan sun bayyana cewa za su kama duk wani mutum ko ƙungiya da ta ci gaba da shirya taron duk da umarnin haramta taron.

  • 2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
  • Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

Mai magana da yawun rundunar, DSP Mansir Hassan, ya ce bincike da rahotannin sirri sun nuna cewa “wasu miyagu na shirin fakewa da taron domin tayar da fitina da haddasa tashin hankali da kuma tayar da rikici a jihar.”

Rundunar ta kuma bayyana cewa lokutan taron sun yi karo da zaɓen fidda gwani na wasu jam’iyyun siyasa da aka riga aka sanarwa ‘yansanda su kamar yadda dokokin Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) suka tanada.

“INEC ta tsara zaɓen fidda gwani na zaɓen cike gurbi a ranar da aka shirya gudanar da taron Peter Obi, kuma jam’iyyun siyasa sun riga sun sanar da ‘yan sanda kamar yadda doka ta tanada,” in ji sanarwar.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

‘Yan sandan sun ƙara da cewa “taron zai iya hana gudanar da zaɓen fidda gwani a wuraren da aka ware, kuma hakan na iya janyo rikici da tashin hankali.”

Duk da cewa ‘yan ƙasa na da ‘yancin taruwa da nuna ƙauna ga shugabannin siyasa, ‘yan sanda sun ce har yanzu tarukan siyasa a jihar an dakatar da su har sai INEC ta sanar da fara kamfen ɗin siyasa.

Rundunar ta yi kira ga masu shirya taron Obi da su soke taron domin gujewa barazana da zaman lafiya da kuma kauce wa masu garkuwa da mutane.

DSP Hassan ya ce rundunar za ta ɗauki matakin doka kan duk wanda ya saɓa da wannan umarni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaObiPeter ObiTaron ranar haihuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

Next Post

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

Related

sallah
Labarai

Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

5 hours ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

8 hours ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

9 hours ago
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

21 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

21 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

22 hours ago
Next Post
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi

Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi

July 19, 2025
UTME

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

July 19, 2025
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

July 19, 2025
‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

July 19, 2025
Abinci

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

July 19, 2025
sallah

Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

July 19, 2025
Shettima

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

July 19, 2025
Fyade

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

July 19, 2025
APC

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

July 19, 2025
Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.