ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Mayar Wa Da Kotu Motocin Da Aka Dauka A Gidan Matawalle – ‘Yansanda

Jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan jihar, Yazid Abubakar, ya ce an mayar da motocin ne bisa bin umarnin babbar kotun tarayya da ke Gusau.

by Muhammad
2 years ago
Matawalle

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce ta mayar da dukkanin motocin da ta kama daga hannun tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle zuwa kotu.

Wata tattaunawa ta wayar tarho da gidan Telebijin na Channels ya yi ranar Asabar da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Yazid Abubakar, ya ce an mayar da motocin ne bisa bin umarnin babbar kotun tarayya da ke Gusau.

  • ‘Yansanda Sun Kai Samame Gidan Matawalle, Sun Kwace Motoci 40
  • Sakarci Da Talauci Ne Yasa Gwamnatin Zamfara Shiga Gidana Sata- Bello Matawalle

“Eh, rundunar ‘yan sanda ta bi umarnin kotu dangane da mayar da dukkan motocin tsohon gwamna Bello Matawalle,” Cewar Kakakin ‘Yansandan.

ADVERTISEMENT

“Mun mayar da dukkan motocin zuwa harabar babbar kotun tarayya da ke Gusau, kamar yadda nake magana da ku yanzu, babu wata mota guda da ke hannun ‘yan sanda.”

A ranar 15 ga watan Yuni, mai shari’a Aliyu Bappa na babbar kotun tarayya Gusau ya umurci dukkanin jami’an tsaro da ke da ruwa da tsaki wajen kwashe motocin daga gidajen Matawalle na Gusau da Maradun da su dawo da su cikin sa’o’i 48.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Kotun ta kuma bayar da umarnin dakatar da wadanda ake kara a karar da Matawalle ya shigar a gaban kotu daga daukar wani mataki na gaba dangane da lamarin.

Wadanda suka amsa karar sun hada da Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nijeriya da hukumar ‘yan sandan Nijeriya da kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da kuma hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC).

Gidan Talabijin na Channels ya ziyarci babbar kotun tarayya da safiyar Lahadi domin tabbatar da wannan umarnin inda ya rawaito cewa motoci 29 ne kawai ke harabar kotun har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

Sai dai majiyoyi sun ce har yanzu wasu motocin na nan a sansanin ‘yan sanda ana sa ran za su isa Gusau a yau Lahadi ko kuma safiyar Litinin.

Sai dai har yanzu tsohon gwamnan bai tabbatar da ko an dawo da motocin ba, har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

A baya dai gwamnatin jihar Zamfara ta ce an kwato fiye da motoci 40 da suka hada da motocin hana shigar harsashi guda uku da kuma SUV guda takwas daga gidajen tsohon gwamnan biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS
Labarai

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
Next Post
Mata Sun Cancanci Samun Karin Mukamai A Gwamnati — Remi Tinubu

Mata Sun Cancanci Samun Karin Mukamai A Gwamnati — Remi Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.