ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Dakatar Da Harajin Tsaron Intanet Kan Hada-hadar Kudade

by Sulaiman
2 years ago
Amurka

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da harajin nan da aka ƙaƙaba wa masu ajiya a banki na tallafin tsaron yanar gizo.

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ne ya bayyana shigo da harajin kan kuɗaɗen da jama’a da kamfanoni ke turawa, wanda hakan ya haifar da ce-ce-ku-ce.

  • Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura
  • Ba Za Ta Saɓu Ba, Mun Maka CBN A Kotu Kan Janye Wa Mutane Kuɗaɗensu A Asusunsu – Ƙungiyoyi

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana matakin da gwamnatin ta ɗauka a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a Fadar Gwamnati da ke Abuja ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Ya ce ana yin nazari kan shirin. “Matsayin gwamnati shi ne an dakatar da wannan shirin. An ɗage shi. Matsayin gwamnati kenan a yanzu. Ana sake sabon nazari a kan sa.
“An maganar sosai a taron Majalisar (FEC) a jiya. Kun san cewa majalisar ta yau (taron) an ɗora ne kan na jiya,” inji ministan.

Ya ƙara da cewa: “Don haka, zan iya gaya maku cewa an dakatar da harajin tsaron yanar gizo. Gwamnati na sake tunani a kan sa.”

LABARAI MASU NASABA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

A ranar 6 ga watan Mayu ne Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya umarci bankuna, masu gudanar da hada-hadar kuɗi ta wayar salula, da masu ba da sabis na biyan kuɗi da su aiwatar da wannan harajin kamar yadda yake ƙunshe a cikin Dokar 2024 ta Laifin Yanar Gizo (Hanawa, Rigakafi, da sauran su) (gyara).

An tsara za a riƙa biyan harajin kashi 0.5 cikin ɗari kan duk kuɗin da mutum ya tura wa wani. Za a aika da kuɗaɗen ne zuwa Asusun Ajiyar Tsaron Yanar Gizo na Ƙasa wanda Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA) ke shugabanta.

Sai dai matakin ya fusata mutane matuƙa, lamarin da ya sa ake kira da a dakatar da shi.

A makon da ya gabata ma Majalisar Wakilai ta buƙaci CBN da ya janye umarnin da ya ba bankuna da su fara aiwatar da harajin, inda ta bayyana hakan a matsayin “shubuha”.

Wannan matakin na gwamnati ya kasance a matsayin martani ga wani ƙudiri kan buƙatar gaggawa na dakatarwa da kuma gyara aiwatar da harajin tsaron yanar gizo da ɗan majalisa Kingsley Chinda ya gabatar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi
Hotuna

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Beijing Na Gaggauta Matakan Amfani Da Motoci Masu Aiki Da Wutar Lantarki Da Aka Samar Ta Makamashi Mai Tsabta

Beijing Na Gaggauta Matakan Amfani Da Motoci Masu Aiki Da Wutar Lantarki Da Aka Samar Ta Makamashi Mai Tsabta

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.