• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yar Shekara 13 Ta Haddace Tare Da Rubuta Alkur’ani A Katsina

An Yi Bikin Karrama Ta A Ranar Asabar

by Sadiq
3 years ago
in Dausayin Musulunci, Manyan Labarai
0
‘Yar Shekara 13 Ta Haddace Tare Da Rubuta Alkur’ani A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata yarinya ‘yar shekara 13 mai suna Zuwaira Ahmed daga kauyen Kagara a Ƙaramar Hukumar Kafur a Jihar Katsina, ta haddace tare da rubuta cikakken Alkur’ani mai girma.

Da ya ke jawabi a wajen bikin karrama yarinyar a yau Asabar, Hakimin Mahuta, Bello Abdulkadir, ya bayyana farin cikinsa da wannan ci gaba da aka samu.

  • Mutane 20 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Oyo
  • Zan Yi Iyakar Kokarina Wajen Bunkasa Karamar Hukuma Garko A Jihar Kano -Salisu Musa Sarina

Ya bayyana cewa, wannan babbar nasara ce ga al’umma, da ma jihar baki daya, musamman a bangaren ilimin addinin Musulunci.

Abdulkadir, ya kuma yaba wa iyaye, malamai da sauran shugabannin al’umma kan yadda suke kula da tarbiyyar ‘ya’yansu yadda ya kamata, yana mai kira gare su da su ci gaba da yin hakan.

Danejin Katsina, ya bai wa sarakunan jihar tabbacin ci gaba da bada goyon baya ga duk wani abu da ya shafi addinin musulunci, domin ci gaban yankin baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Shugaban karamar hukumar Kafur, Garba Kanya, ya yaba da kwazon yarinyar tare da bada tabbacin tallafa mata a matakin karatunta na sakandire da manyan makarantu.

Shugaban makarantar ta, Madrasatul Tahfiz, Sheikh Sani Kagara, ya ce an kafa makarantar ne da nufin yin tasiri na ingantaccen ilimin addinin Musulunci a tsakanin matasa a cikin al’umma.

A cewarsa, yarinyar ta haddace Alkur’ani ne a cikin shekaru hudu, kuma ya danganta nasarar da ta samu ga goyon bayan iyayenta da jajircewar malamanta a makaranta.

A nasa jawabin, mahaifin hafizar, Ahmed Sani, ya yaba da duk tallafin da aka ba shi da ‘yarsa, inda ya yi kira ga iyaye da su bar ‘ya’yansu su samu ilimin addinin musulunci da na boko.

Ya kuma ba da tabbacin ci gaba da ba ta goyon bayan da ya dace don kuma ta ci gaba da karatun ta na boko, inda ya ce a halin yanzu tana makarantar firamare a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yar Shekara 13Addinin MusulunciAlkur'ani Mai GrimaHaddaKyauta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 20 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Oyo

Next Post

Annobar Tura Yara Mata Aikatau!

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

7 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

9 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

15 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

16 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

19 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

1 day ago
Next Post
Annobar Tura Yara Mata Aikatau!

Annobar Tura Yara Mata Aikatau!

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.