ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yara Miliyan 1 Ke Mutuwa Duk Shekara A Farkon Watansu Na Haihuwa A Nijeriya – UNICEF

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Yara

Asusun kula da ilimin yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya ce, a kalla yara miliyan daya ke mutuwa a kowace shekara a Nijeriya a cikin watansu na farko da haihuwa, lamarin da ke nuni da cewa kaso 10 cikin 100 a duniyance.

Jami’in lafiya na ofishin UNICEF da ke Bauchi, Oluseyi Olosunde, shi ne ya shaida hakan a wani taron kara wa juna sani na wuni guda da aka shirya wa ‘yan jarida kan yawan mace-macen yara a Bauchi, Gombe, Taraba da ya gudana a Jos ta jihar Filato.

  • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Biyan Bashin Waɗanda Aka Tsare A Gidan Gyaran Hali
  • Batun Tuhumar Ƙananan Yara Da Laifin Shirya Juyin Mulki

Ya ce bisa adadin mace-macen da ke faruwa a Nijeriya, ya nuna cewa, yara miliyan 1 ke mutuwa a farkon watansu na farko a duniya.

ADVERTISEMENT

Jami’in ya ce a kowace rana, Nijeriya ta rasa yara ‘yan kasa da shekaru biyar su 2,300, inda ya ce, mafi yawan wadannan mace-macen suna wakana ne a yankunan karkara, inda kuma a kalla yara 157 ke mutuwa a yankunan karkara kullum.

Ya kara da cewa bisa abubuwan da suke janyo mutuwar yaran sun hada da talauci da karancin asibitocin kula da yara, wanda ke janyo rashin samun kulawar kiwon lafiya.

LABARAI MASU NASABA

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Ya ce, sauran hanyoyin da suke janyo mutuwar sun hada da haihuwa bisa kan al’adar da aka saba, rashin ilimi, karancin abinci mai gina jiki da karancin wayarwa.

A nata jawabin, Dakta Ruth Adah, wata kwararriya a asibitin koyarwa na jami’ar Jos, ta lura kan cewa akwai bukatar a tashi tsaye wajen amfani da dokokin kariya ga rayuwar yara domin rage yawaitar mace-macensu da ake fuskanta.

Ta ce, duk da Nijeriya ana yawan samun mace-macen yara, amma Jihar Bauchi, Gombe da Taraba su ne kan gaba wajen samun mace-macen yara kanana a fadin Nijeriya.

Adah ta jinjina wa UNICEF bisa shirya taron bita wa ‘yan jaridan, tana mai cewa wannan ya zo a kan gaba domin samun dama da hanyoyin wayar wa jama’a da gwamnatoci kai, kan yadda a dauki matakan da suka dace wajen rage yawaitar mace-macen yara a cikin al’umma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Next Post
 ‘Yan Majalisar Nijeriya Na Matsin Lamba Ga Jami’an Gwamnati Wajen Yin Cushe A Kasafin Kudi –Jega

 ‘Yan Majalisar Nijeriya Na Matsin Lamba Ga Jami’an Gwamnati Wajen Yin Cushe A Kasafin Kudi –Jega

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.