ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Majalisar Nijeriya Na Matsin Lamba Ga Jami’an Gwamnati Wajen Yin Cushe A Kasafin Kudi –Jega

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Nijeriya

Tsohon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya bayyana cewa ‘yan majalisan Nijereiya na matsinlamba ga jami’an gwamnati wajen yin cushe a kasafin kudi domin cimma burinsu.

Farfesa Jega ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar a taron ‘Horar da canjin dabi’un cin hanci da ’, wanda hukumar yaki da cin hanci da rashawa da sauran laifuka (ICPC) ta shirya a Abuja.

  • Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi
  • Shugaban Majisar Dattawa Ya Yi Wa Daurarru 15 Afuwa Daga Gidan Yari Na Yobe

Ya bayyana cin hanci da rashawa a ma’aikatun gwamnati a matsayin babban cikas ga ci gaban Nijeriya tare da sukar matsalolin da manyan jami’ai ke fuskanta musamman daga bangaren majalisa.

ADVERTISEMENT

“Akwai mutanen da suke tursasa jami’an gwamnati su gudanar da aikinsu, ko mai kyau ko kuma akasin haka. Wadannan mutane za su iya kasancewa ‘yan majalisa ko kuma ba ‘yan majalisa ba,” in ji shi.

Ya tunatar da yadda wasu ‘yan majalisar suka yi yunkurin yin tasiri a kan kasafin kudi da kuma tabbatar da kwangiloli, wanda hakan ya kawo cikas ga kokarin jami’an gwamnati na tabbatar da gaskiya.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Da yake waiwayar zamansa a hukumar ta INEC, ya bayyana hakan a matsayin za zakaran gwaji dafi ganin yadda ‘yan majalisar ke takurawa kan kasafin kudin hukumar da kwangiloli a kullum.

“Kaurace wa matsinlambar yana bukatar jajircewa. Yana da muhimmanci a kaurace masa don bin bin doka da ka’idojin Nijeriya.”

Ya kuma soki al’adar cin hanci da rashawa da ta yadu a sassan gwamnati tare da yin kira da a sake fasalin hukumomi.

Ana dai zargin majalisar dokokin kasar da cin hanci da rashawa daban-daban da suka hada da karkatar da kasafin kudi na tsawon shekaru. Gudanar da ayyukan mazabu babban misali ne kan hakan.

Wasu rahotannin da hukumar ICPC ta fitar sun bankado yadda ‘yan majalisar dokokin kasar ke amfani da kudaden gwamnati tare da hadin gwiwar hukumomin gwamnati ta hanyar kashe kasafin kudin kasa na ayyukan mazabu wadanda galibinsu ba su ba a aiwatar da su ba.

Rahotannin da ke bin diddigin ayyukan mazabar da ICPC ta fitar sun bankado wasu laifukan da ake zargin ‘yan majalisar tarayya na aikatawa tare da hadin gwiwar wasu jami’an ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya.

Farfesa Jega ya jaddada bukatar samun kwakkwaran jagoranci wajen magance cin hanci da rashawa.

Ya kara da cewa idan ba a samu cikakken sauye-sauye a bangaren shari’a da sauran manyan cibiyoyi ba, cin hanci da rashawa zai ci gaba da wanzuwa. Ya ce al’adar cin hanci da rashawa ta kafu ne ta hanyar lakabin gargajiya da ake ba wa jami’an gwamnati, wanda a ganinsa yana karfafa yin biyayya da ayyukan da ba su dace ba.

“Da zarar an fara yin shit un yana karami, yana ci gaba da girma, ina ba da shawarar sake duba yadda tsarin aikin gwamnati ya tasiri.”

Ya kuma jaddada bukatar karfafa kariya ga masu fallasa bayanan sirri da inganta hanyoyin karfafawa mutane kai rahoton cin hanci da rashawa.

Jega ya bayar da shawarwari da suka hada da kakkarfan kariya ga masu fallasa bayanai, hada kai da matasa, da habaka horar sabbin dabi’un shugabanci.

Da yake goyon bayan bayanan Jega, shugaban ICPC, Musa Aliyu ya bukaci shugabannin ma’aikatun tarayya, sassan da hukumomi da su karfafa tsarin yaki da cin hanci da rashawa.

Ya yi gargadin cewa rashin yin hakan zai sa a gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.

“Ba za a iya kididdiga barnar da cin hanci da rashawa ya yi wa ma’aikatan gwamnati da kuma al’ummarmu ba,” in ji Aliyu, yana mai bukatar jajircewa wajen yaki da cin hanci da rashawa.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.