ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Tuhumar Ƙananan Yara Da Laifin Shirya Juyin Mulki

by Ra'ayinmu
2 years ago
Yara

A kwanakin baya ne, kafafen yada labarai na cikin  gida da na kasashen waje suka kasance cike da labaran gurfanar da kananan yara da babbar kotun tarayya ta yanke masu hukuncin cin manar kasa saboda gudanar da zanga-zangar kawo karshen rashin gudanar da shugabanci na gari a Nijeriya da kuma sauran aikata laifuka.

Wani babban abin takaici shi ne, yadda kafafen yada labarai na kasashen waje suka wallafa cewar, gwamnatin kasar nan, za ta yankewa su yaran 29 hukuncin kisa saboda gudanar da halin yunwar da aka shiga a kasa.

  • Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa
  • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Biyan Bashin Waɗanda Aka Tsare A Gidan Gyaran Hali

Sai dai kuma, wasu kwararrun Lauyioyi da kungiyoyin kare rajin ‘yancin ‘yan Adam a kasar, sun fito karara sun yi tir da kama yaran da mahukuntar kasar suka yi kan gudanar da zanga-zangar, musamman ma idan aka yi la’akari da yadda wasu daga cikin yaran da aka gurfanar a gaban babbar kotun tarayya bayan an gurfanar da su a gaban kotun domin bukatar bayar da belinsu.

ADVERTISEMENT

Kazalika ma, lamarin ya kuma kara yamutsewa hakan ya biyo bayan zargin da aka yi na cewa, a lokacin da suke tsare a hannun ‘yan sanda, sun ci zarafin su, wadanda kuma ‘yan sandan suka mayar da su tamkar wadanda suka aikata wani babban laifi.

Makomar wadannan yaran dai, tasa tunawa da zanga-zangar #EndSARS wadda wasu jami’an tsaro suka yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin masu zanga-zangar a lokacin da suke kan yin zanga-zangar.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Me yiyuwa sukar da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta sha ne, ya tilasata shi bayar da umarni nan take, da a saki yaran a kuma gaggauta mika su ga iyayensu.

A nan, muna jinjinawa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan ceto rayuwar yaran daga hannun jami’an tsaron, musamman ma  idan aka yi la’akari da irin wahalar da suka sha a hannun ‘yansanda.

A bisa tunanin, tun da farko bai kamata ma ace ‘yan sandan sun kama yaran ba, domin yaran dai, sun yi zanga-zangar ce kan kuncin rayuwa.

Zaman da yaran suka yi a kulle, hakan ya nuna cewa, an barsu ne a cikin yunwa da kasancewa a cikin rashin lafiya don kawai sun gudanar da zanga-zangar fargar da gwamnati kan ci gaba da kasancewar talakawan kasar, a cikin kangin talauci.

Kwanci tashi, irin juyin juya hali da ya auku a kasar Faransa, ya janyo kifar da masarautar garjiya ta kasar, musamman ma, ba wai don samun yawan talauci ba, amma saboda irin mulkin gurguzu da masarautar ke yiwa ‘yan kasar.

Kazalika ma, kasar Rasha ba wai an kifar da gwamnatin kasar ne da makamin kari dangi ne ba, abin ya kawo karshen shugabannin  kasar ba, amma boren da ‘yan kasar suka gudanar ne, ya kawo karshen shugabancin mahukuntar kasar, ya biyo bayan jefa rayuwarsu a cikin kangin rikcewar rayuwa.

Namu ra’ayin a nan shi ne, akasarin kasashe ba su koyon darasi a kan kuskuren da wasu kasashen suke tabkawa.

Abinda ke faruwa a Nijeriya shi ne, kusan matakan da bangaren gwamnatoci uku na kasar ke yi, ba su daukar kwararan matakan da suka dace.

Duk kasar da ta kasance kayan abinci da sauran kayan amfanin yau da kullum sun fi karfin talakan kasar, amma masu rike da madabun iko na siyasa, suna yin wandaka da watanda da kudaden gwamnati yadda suke so, suna kuma barin ‘ya’yan talakawa a cikin kangin halin yunwa, wannan babban abin bakin ciki ne.

Ra’ayinmu a nan irin yadda yaran suka tsinci kansu a cikin cin zarafin gwamnatin su, wadda ya kamata ta nuna cewa, mulkin dimokiradiyya ne ake gudanarwa a kasar hakan kuma ya nuna cewa, tamkar ana gudanar da mulkin mallakar Fir’aunanci ne a kasar.

A matsayin a wannan jaridar, mun nuna taikaicin mu a kan irin halin da yaran suka tsinci kansu a lokacin da aka tsare su, wanda kuma jami’an tsaro suka dauke su tamkar wasu masu mugun hadari a cikin alumma.

A bisa tunanin mu, irin wannan halin da aka jefa yaran a ciki, hakan zai iya juya tunanin su zuwa rungumar munanan dabi’u.

Ya zama wajbi mu ankarar da mahukunta don su gane cewa, ya kamata su san yadda za su rinka tafiyar da yara a duk lokacin gudanar da wata zanga-zanga, kamar dai irin ta #EndBadGobernance.

Yara
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Matsalar Ɓacewar Gandun Dazukan Nijeriya

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Dambarwar Shirin Tinubu Na Yi Wa Dokar Haraji Kwaskwarima…

Dambarwar Shirin Tinubu Na Yi Wa Dokar Haraji Kwaskwarima...

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.