• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

by Bello Hamza
2 years ago
in Bakon Marubuci
0
Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana ‘yan makonni zuwa babban zaben 2023, fagen siyasar kasar nan yana kara zafafa inda manyan jam’iyyun biyu na ci gaba da yi wa juna yarfe, kazafi da sharin aikata cin-hanci da almundahana a tsakaninsu.

Bangaren dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar suke jifar juna da wadannan zarge-zargen.

  • Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   
  • Karin Bayani Kan Harin Bom Din Da Ya Kashe Fulani 39 A Nasarawa — Ganau

Jam’iyyar APC ce ta fara harbo mizal din. Kusan mako daya daya wuce ne kwamitin yakin neman zaben Tinubu/Shettima ya nemi a gaggauta kamawa tare da hukunta dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar saboda zargin badakalar kudade da suke zargin ya aikata tare kuma da aikata manyan laifuka.

Kungiyar ta bayyana haka ne a taron manema labarai da ta kira a Abuja inda ta kara da cewa, Atiku bashi da wani kariya na tsarin mulki da zai hana a kama shi tare da hukunta shi, shugabanin bangaren watsa labarai a kwamitin yakin neman zaben  Tinubu da suka hada da Dele Alake, Festus Keyamo, Bayo Onanuga, Femi Fani-Kayode, da kuma Idris Mohammed suka jagoranci taron manema labaran, sun kuma nemi Atiku ya gaggauta yin murabus daga takarar shugabancin kasa  da yake yi tare da ba wa al’ummar Nijeriya hakuri a kan zargin da ake yi masa na karkatar da kudaden al’umma zuwa aljihunsa.

Sun kuma yi alkawarin garzayawa kotu don dakatar da takarar da yunkurin da tsohon mataimakin shugaban kasar yake yi na zama shugaban kasa a zaben da za a gudanar wata mai zuwa. Wannan zargin yana zuwa ne bayan da wani tsohon hadimin Atiku, Mista Michael Achimugu, ya yi zargin cewa, Atiku ya yi amfani da shirin nan na sayen motocin SPB wajen kwasar kudade daga tsohon Gwamnan Jihar Filato Joshua Dariye wanda kotu ta daure saboda badakalar kudaden kare zaizayar kasa na Jihar Filato. Tuni dai Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi masa afuwa. A lokacin da Atiku yake mataimakin shugaban Nijeriya daga 1999 zuwa 2007, Dariye na a matsayin gwamna ne a daidai lokacin.

Labarai Masu Nasaba

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

A ranar Lahadi 22 ga watan Janairu 2023, bangaren kwamitin yakin neman zaben Atiku suka mayar da nasu martanin, inda suka bukaci hukumar yaki da fataucin miyagin kwayoyi NDLEA da hukumar EFCC su gaggauta kama dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu. Bayanin haka yana kunshe ne a jawabin da mambobin kwamitijn yakin neman zaben jam’iyyar PDP suka yi a ta bakin Bashorun Dele Momodu, Daniel Bwala, Mista Paul Ibe da kuma mataimaki na musamman ga Atiku a kan harkar yada labarai, Phrank Shaibu a ganawar da suka yi manema labarai.

A cikin jawabin su, Shaibu ya lura da cewa, Nijeriya na fuskantar wai yanayi da ya kamata a yi takatsanstan wajen zaban wanda zai zama shugaban kasa nag aba , kuma duk wani kuskure da za a yi zai iya zama bala’i ga kasa baki daya. Ya kara da cewa,“Nijeriya na fuskantar matsalolin da suka hada da na ‘yan bindiga, garkuwa da mutane da sauran miyagun ayyukan ta’addanci wadanda kuma suke da alaka da tu’ammali da miyagun kwayoyi. “A saboda haka zai iya zama tashin hankali in aka zabi wanda rayuwarsa ke tattare da badakalar harkar kwaya da safarar ta.”

Ya bayyana cewa, Tinubu na fuskantar badakalar Dala 460,000 wanda ake zargin ya samu ne daga badakalar safarar miyagun kwayoyi a kasar Amurka, ya kuma kamata a kara zurfafa bincike don gano cikakiyyar gaskiyar lamarin. “A kan haka muna kira ga hukumar NDLEA su gagaggauta kama Bola Ahmed Tinubu su kuma tabbatar da hukunta shi.

Wananan takaddamar da yarfe a tsakanin manyan jam’iyyun kasar nan abu ne da zai iya tayar da kura a sararin samaniyar harkokin siyasar kasar nan kamar yadda kungiyar Afenifere ta ankarar ta bakin sakatarenta na kasa Kwamrade Jare Ajayi, amma kuma wannan yana kara fitowa ne da lamarin cin-hanci da rashawa matsayin wani abin da yakamata ya zama a kan gaba a cikin abubuwan da yakamata a rika tattauanwa a fagen yakin neman zabe a tsakanin jam’iyyun kasar nan.

Abin lura a nan shi e dukkan jam’iyyun kasar masu neman shugabancin kasar na ikiirarin za su jagoranci yaki da cin-hanci da rashawa in kai ga ci.

Za a iya fahimtar yadda matsalar cin-hanci da rashawa ta yi katutu a harkar kasar nan in aka lura da cewa, kungiyar ‘Transparency International (TI)’ ta ayyana Nijeriya a matsayin kasar da ke a kan gaba a cikin kassashen da aka fi cin-hanci da rashawa a duniya, saboda haka tabbas ya kamata lamarin cin-hanci da rashawa ya zama a kan gaba kuma ma’auni na alkawurran da manya jam’iyyumu za su yi amfani da su wajen yakin neman zaben da ake yi a halin yunzu a shirye-shiryen fuskantar zaben 2023.

Yana da matukar muhimmanci hukumomin da abin ya shafa su tabbatar da bincikar zarge-zarge biyu da bangarorin suka yi wa junansu. Bai kamata a yi watsi da zarge-zargen ba.

Ganin iri wannan zarge-zarge masu tayar da hankali ne a kan manyan ‘yan takarar shugabancin kasar a halin yanzu al’amura duk sun koma a hannun ‘yan Nijeriya masu dauke da katin zabe, ya kamata su yi karatun ta natsu su zabawa kasar nan wanda ya fi dama-dama don daga dukkan alamu tsakanin manyan ‘yan takarar shugabancin kasar nan duk gautar ja ce.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SiyasaYarfeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Daga 2016 Zuwa 2020, An Kashe Dala Biliyan 6 Wajen Shigo Da Alkama -CBN

Next Post

An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

Related

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

2 weeks ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

4 weeks ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

1 month ago
Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

2 months ago
Waraka Daga Bashin Ketare
Bakon Marubuci

Waraka Daga Bashin Ketare

3 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [21]

3 months ago
Next Post
An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

LABARAI MASU NASABA

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.