• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

by Bello Hamza
3 years ago
in Bakon Marubuci
0
Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana ‘yan makonni zuwa babban zaben 2023, fagen siyasar kasar nan yana kara zafafa inda manyan jam’iyyun biyu na ci gaba da yi wa juna yarfe, kazafi da sharin aikata cin-hanci da almundahana a tsakaninsu.

Bangaren dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar suke jifar juna da wadannan zarge-zargen.

  • Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   
  • Karin Bayani Kan Harin Bom Din Da Ya Kashe Fulani 39 A Nasarawa — Ganau

Jam’iyyar APC ce ta fara harbo mizal din. Kusan mako daya daya wuce ne kwamitin yakin neman zaben Tinubu/Shettima ya nemi a gaggauta kamawa tare da hukunta dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar saboda zargin badakalar kudade da suke zargin ya aikata tare kuma da aikata manyan laifuka.

Kungiyar ta bayyana haka ne a taron manema labarai da ta kira a Abuja inda ta kara da cewa, Atiku bashi da wani kariya na tsarin mulki da zai hana a kama shi tare da hukunta shi, shugabanin bangaren watsa labarai a kwamitin yakin neman zaben  Tinubu da suka hada da Dele Alake, Festus Keyamo, Bayo Onanuga, Femi Fani-Kayode, da kuma Idris Mohammed suka jagoranci taron manema labaran, sun kuma nemi Atiku ya gaggauta yin murabus daga takarar shugabancin kasa  da yake yi tare da ba wa al’ummar Nijeriya hakuri a kan zargin da ake yi masa na karkatar da kudaden al’umma zuwa aljihunsa.

Sun kuma yi alkawarin garzayawa kotu don dakatar da takarar da yunkurin da tsohon mataimakin shugaban kasar yake yi na zama shugaban kasa a zaben da za a gudanar wata mai zuwa. Wannan zargin yana zuwa ne bayan da wani tsohon hadimin Atiku, Mista Michael Achimugu, ya yi zargin cewa, Atiku ya yi amfani da shirin nan na sayen motocin SPB wajen kwasar kudade daga tsohon Gwamnan Jihar Filato Joshua Dariye wanda kotu ta daure saboda badakalar kudaden kare zaizayar kasa na Jihar Filato. Tuni dai Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi masa afuwa. A lokacin da Atiku yake mataimakin shugaban Nijeriya daga 1999 zuwa 2007, Dariye na a matsayin gwamna ne a daidai lokacin.

Labarai Masu Nasaba

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

A ranar Lahadi 22 ga watan Janairu 2023, bangaren kwamitin yakin neman zaben Atiku suka mayar da nasu martanin, inda suka bukaci hukumar yaki da fataucin miyagin kwayoyi NDLEA da hukumar EFCC su gaggauta kama dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu. Bayanin haka yana kunshe ne a jawabin da mambobin kwamitijn yakin neman zaben jam’iyyar PDP suka yi a ta bakin Bashorun Dele Momodu, Daniel Bwala, Mista Paul Ibe da kuma mataimaki na musamman ga Atiku a kan harkar yada labarai, Phrank Shaibu a ganawar da suka yi manema labarai.

A cikin jawabin su, Shaibu ya lura da cewa, Nijeriya na fuskantar wai yanayi da ya kamata a yi takatsanstan wajen zaban wanda zai zama shugaban kasa nag aba , kuma duk wani kuskure da za a yi zai iya zama bala’i ga kasa baki daya. Ya kara da cewa,“Nijeriya na fuskantar matsalolin da suka hada da na ‘yan bindiga, garkuwa da mutane da sauran miyagun ayyukan ta’addanci wadanda kuma suke da alaka da tu’ammali da miyagun kwayoyi. “A saboda haka zai iya zama tashin hankali in aka zabi wanda rayuwarsa ke tattare da badakalar harkar kwaya da safarar ta.”

Ya bayyana cewa, Tinubu na fuskantar badakalar Dala 460,000 wanda ake zargin ya samu ne daga badakalar safarar miyagun kwayoyi a kasar Amurka, ya kuma kamata a kara zurfafa bincike don gano cikakiyyar gaskiyar lamarin. “A kan haka muna kira ga hukumar NDLEA su gagaggauta kama Bola Ahmed Tinubu su kuma tabbatar da hukunta shi.

Wananan takaddamar da yarfe a tsakanin manyan jam’iyyun kasar nan abu ne da zai iya tayar da kura a sararin samaniyar harkokin siyasar kasar nan kamar yadda kungiyar Afenifere ta ankarar ta bakin sakatarenta na kasa Kwamrade Jare Ajayi, amma kuma wannan yana kara fitowa ne da lamarin cin-hanci da rashawa matsayin wani abin da yakamata ya zama a kan gaba a cikin abubuwan da yakamata a rika tattauanwa a fagen yakin neman zabe a tsakanin jam’iyyun kasar nan.

Abin lura a nan shi e dukkan jam’iyyun kasar masu neman shugabancin kasar na ikiirarin za su jagoranci yaki da cin-hanci da rashawa in kai ga ci.

Za a iya fahimtar yadda matsalar cin-hanci da rashawa ta yi katutu a harkar kasar nan in aka lura da cewa, kungiyar ‘Transparency International (TI)’ ta ayyana Nijeriya a matsayin kasar da ke a kan gaba a cikin kassashen da aka fi cin-hanci da rashawa a duniya, saboda haka tabbas ya kamata lamarin cin-hanci da rashawa ya zama a kan gaba kuma ma’auni na alkawurran da manya jam’iyyumu za su yi amfani da su wajen yakin neman zaben da ake yi a halin yunzu a shirye-shiryen fuskantar zaben 2023.

Yana da matukar muhimmanci hukumomin da abin ya shafa su tabbatar da bincikar zarge-zarge biyu da bangarorin suka yi wa junansu. Bai kamata a yi watsi da zarge-zargen ba.

Ganin iri wannan zarge-zarge masu tayar da hankali ne a kan manyan ‘yan takarar shugabancin kasar a halin yanzu al’amura duk sun koma a hannun ‘yan Nijeriya masu dauke da katin zabe, ya kamata su yi karatun ta natsu su zabawa kasar nan wanda ya fi dama-dama don daga dukkan alamu tsakanin manyan ‘yan takarar shugabancin kasar nan duk gautar ja ce.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SiyasaYarfeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Daga 2016 Zuwa 2020, An Kashe Dala Biliyan 6 Wajen Shigo Da Alkama -CBN

Next Post

An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

Related

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan
Bakon Marubuci

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

4 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

6 days ago
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
Bakon Marubuci

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

2 weeks ago
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
Bakon Marubuci

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

2 months ago
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
Bakon Marubuci

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

2 months ago
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

2 months ago
Next Post
An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.