• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro A Nijeriya: Akwai Bukatar Daukar Kwakkwaran Mataki

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Matsalar Tsaro A Nijeriya: Akwai Bukatar Daukar Kwakkwaran Mataki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya ta sake samun kanta a cikin halin tashin hankali, tsoro da alhini, a yayin da rahotanni suke nuna cewa, ‘yan ta’adda dauke da muggan makamai sun yi awon gaba da daruruwan dalibai ‘yan makaranta a wasu jihohin kasar nan, wannan  shi ya dawo da hannun agogo baya a kokarin da gwamnatoci a dukkan matakai suke yi na samar da tsaro a kasar nan.

A kwanakin baya ne ‘yan ta’adda suka sace dalibai 280 da Malaman su daga makarantar LEA da ke garin Kuriga, karamar Hukumar Birnin gwari ta Jihar Kaduna.

  • Ɗiawara Ya Fice Daga Tawagar Faransa Bayan An Hana ‘Yan Wasa Yin Azumi
  • Sin Za Ta Inganta Zamanintarwa Bisa Bunkasuwa Mai Inganci Don Ba Da Karin Karfi Ga Ci Gaban Duniya

Haka kuma wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun kai hari a yankin Buda da ke karamar hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna inda suka yi nasarar sace mutum 61.

Duk a ‘yan kwanakin nan, sai gashi kuma ‘yan ta’addar Boko Haram sun yi awon gaba da mata 200 a yankin Gamboru-Ngala da ke karamar hukumar Dikwa ta Jihar Borno.

Rahotannin sun nuna cewa, matan da aka sace na daga cikin ‘yan gudun hijira ne da ayyukan ‘ta’addanci ya raba su da muhallansu a yankin Arewa maso gabas, an kuma sace su ne a yayin da suka shiga daji don neman itacen dafa abinci.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Har ila yau mun samu rahoton kashe mutum 50 ciki har da iyalai 7 a harin da ‘yan ta’addan suka kai yankin Gbagir da ke karamar hukumar Ukum ta Jihar Benuwai.

A daidai lokacin da ‘yan ta’addar ke cin karensu babu babbaka sai kuma gashi sun kai hari  a kauyen Gidan Bakuso da ke karamar hukumar Gada can Jihar Sakkwato, inda can ma suka yi awon gaba da almajirai ‘yan makarantar tsangaya 15 wasu kuma da dama ba a samu labara inda suke ba har zuwa yanzu.

A ra’ayin wannan jarida, wadannan ayyuykan ta’addanci ba abin da ya kamata a kawar da kai ba ne; wadannan sun kasance wasu sabbin babi a cikin ayyukan ta’addanci da ya addabi sassan Nijeriya a cikin ‘yan shekarun nan.

Nijeriya ta dade tana dandana kudarta a hannun ‘yan ta’addr  da suke harkokinsu ba tare da wani tsoro ba a sassan Nijeriya.

Wadannan ayyukan garkuwa da mutane da suka sake kunnu kai sun matukar tayar da hankulan al’umma, wadanda suka dade suna sauraron alkawurran masu tafi da kasa na cewa, lallai za a samar masu da tsaro amma kuma har yanzu babu ranar tabbatar da cika wannan alkawarin.

A ra’ayinmu, lokaci ya yi da za a sauya salon da ake amfani da shi a yaki da ta’addanci a Nijeriya. Duk da cewa, gwamnatin Shugaba Bola  Ahmed Tinubu ta gaji wasu daga cikin matsalolin tsaron da ake fuskanta, matsalar da take barazana da kokarin jawo masu zuba jari daga cikin Nijeriya da kuma kasashen waje.

A ra’ayinmu, duk irin abubuwan da Shugaba Tinubu ya shirya gabatarwa na ci gaban kasa, batun samar da tsaro shi ya kamata ya zama a kan sahun gaba don da shi ne tattalin arziki zai karu, musamman ma la’akarin yadda ya tafiyar da tsaro da zaman lafiyar al’ummar kasa, musamman ganin yadda ake kashe mutane da tare da kakkautawa ba.

Matsayar shugaban kasa na kin biyan kudin fansa ga ‘yan ta’adda wannan ma abin a yaba ne. Hakan ya yi daidai da yadda ake tafiyar da irin wannan matsalar a sauran sassan duniya, yana kuma aikawa da sako mai karfi ga su ‘yan ta’addar da ‘yan bindiga na cewa, gwamnati a shirye take da ta murkushe su.

Amma kuma dole gwamnati ta fito da tsari na musamman kan yadda za ta karya alkadarin ‘yan ta’addar ba tare da bata lokaci ba.

Tattaunawa da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga ba zai haifar da da mai ido ba, irin tattaunawar tana kara karfafa kungiyoyin ne kawai da kuma nuna tamkar gwamnati bata da yadda za ta yi.

Muna kara jaddada cewa, bai kamata Nijeriya ta nuna gazawa ba a fafatawarta da ‘yan ta’addar da suka gallaza wa al’umma ba tare da tausaya masu ba. Lokacin da duk wata tattuanawa ta wuce, abin da ake bukata a halin yanzu shi ne fafatawa da gungun masu aikata laifi.

Domin samun wannan nasarar, dole ne Shugaba Tinubu ya karfafa jami’an tsaronmu ta hanyar samar masu da dukkan kayan aiki na zamani daidai da irin wadanda ake amfani da su a kasashe duniya wadanda suka ci gaba.Hakanan kuma a kwai bukatar a karfafa hanyoyin samar da bayanan sirri domin dakile ayyukan ‘yan ta’adda a daidai lokacin da suke shiryawa.

Hakanan kuma ya kamata a yi maganin ainihin  su matsaloli da dalilan da suke taimakawa wajen bunkasar harkokin ta’addanci a Nijeriya wadanda suka hada da talauci, rashin aikin yi ga matasanmu da kuma yadda ake nunawa wasu al’umma wariya a harkokinsu na yau da kullum na kasa.

Ya kamata a samar da ingantaccen tsarin yaki da ta’addanci wanda ya hada da samar da ayyukan bunkasa rayuwar al’umma da suka hada da samar da aikin yi ga matasa, bunkasa bangaren ilimi, kiwon lafiya, da kuma sauraron koke-koken al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 2

Next Post

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

Related

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

46 minutes ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

2 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

12 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

21 hours ago
Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon
Manyan Labarai

Buhari Ba Mutum Ne Mai Son Abun Duniya Ba – Gowon

23 hours ago
Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

1 day ago
Next Post
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.