ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hedikwatar Tsaron Nijeriya Ta Bayyana Sunayen ‘Yan ta’adda 97 Da Ake Nema Ruwa A-jallo

by Muhammad
2 years ago
Nijeriya

Hedikwatar tsaro ta yi kira ga ‘yan Nijeriya da su bayar da bayanan kan wasu ‘yan ta’adda 97 da ake nema ruwa a jallo, wadanda ke haddasa munanan laifuka a kasa.

Darakta mai kula da ayyukan yada labarai na tsaro, Maj.-Gen. Edward Buba ne ya tabbatar da sunaye da hotunan mutanen da aka bayyana ana nema ruwa a jallo a ranar Juma’a.

  • Matsalar Tsaro A Nijeriya: Akwai Bukatar Daukar Kwakkwaran Mataki
  • Tsaron Iyakoki: ACG James Sunday Ya Jagoranci Taron Samar Da Dabarun Aiki A Jos

Idan dai za a iya tunawa, a watan Nuwamban 2022 ne sojoji suka bayyana cewa za a gurfanar da shugabannin ‘yan bindiga 19 tare da bayar da ladan naira miliyan 5 ga duk wanda ya fallasa ‘yan ta’adda don a karfafa guiwar ‘yan Nijeriya su bayar da bayanan yadda za a kai ga kama masu laifin.

ADVERTISEMENT

Sai dai kuma a wannan lokacin ba a bayar da wata kyauta kan bayar da bayanai kan mutane 97 da aka bayyana ana nema ruwa a jallo ba, wadanda suka hada da shugaban kungiyar masu fafutukar neman kafa kasar Biafra, IPOB.

Sunaye da hotunan sun kunshi ‘yan ta’adda daga Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma da kuma masu tayar da kayar baya a Kudu maso Gabas da Arewa ta Tsakiya.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Kimanin mutane 43 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a shiyyar Arewa maso Yamma, daga cikinsu akwai Alhaji Shingi da Malindi Yakubu Boka da Dogo Gide da Halilu Sububu da Ado Aliero da Bello Turji da Dan Bokkolo da Labi Yadi da Nagala da Saidu Idris da Kachalla da Rugga da kuma Sani Gurgu.

Kazalika, an bayyana mutane 33 da ake nema ruwa a jallo a yankin Arewa maso Gabas sakamakon rikicin Boko Haram da kungiyar IS mai da’awar kafa daular musulunci a yammacin Afirka.

Wasu daga cikin ‘yan ta’addar da ake nema ruwa a jallo sun hada da Abu Zaida da Modu Sulum da Baba Data da Ahmad da Sani Teacher da Baa Sadiq da Abdul Saad da Kaka Abi da Mohammad Khalifa da Umar Tella da Abu Mutahid da Malam Mohammad da kuma Malam Tahiru Baga da kuma Uzaiya da Ali Ngule.

A halin da ake ciki dai an bayyana cewa ana zargin masu tada kayar baya 21 da kuma masu aikata laifuka a yankin Kudu maso Gabas da Arewa ta Tsakiya.

Wadanda ake tuhuma da laifin sun hada da Simon EkpaEkpa da Chika Edoziem da Egede da Zuma da ThankGod da Gentle da Flavour da Mathew da David Ndubuisi da High Chief Williams Agbor da Ebuka Nwaka da Friday Ojimka da Obiemesi Chukwudi aka Dan Chuk da David Ezekwem Chidiebube da Amobi Chinonso Okafor mai inkiyar Temple da dau sauransu.

Nijeriya
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Alamomin Kansar Mama Ta Maza

Alamomin Kansar Mama Ta Maza

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.