ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hedikwatar Tsaron Nijeriya Ta Bayyana Sunayen ‘Yan ta’adda 97 Da Ake Nema Ruwa A-jallo

by Muhammad
2 years ago
Nijeriya

Hedikwatar tsaro ta yi kira ga ‘yan Nijeriya da su bayar da bayanan kan wasu ‘yan ta’adda 97 da ake nema ruwa a jallo, wadanda ke haddasa munanan laifuka a kasa.

Darakta mai kula da ayyukan yada labarai na tsaro, Maj.-Gen. Edward Buba ne ya tabbatar da sunaye da hotunan mutanen da aka bayyana ana nema ruwa a jallo a ranar Juma’a.

  • Matsalar Tsaro A Nijeriya: Akwai Bukatar Daukar Kwakkwaran Mataki
  • Tsaron Iyakoki: ACG James Sunday Ya Jagoranci Taron Samar Da Dabarun Aiki A Jos

Idan dai za a iya tunawa, a watan Nuwamban 2022 ne sojoji suka bayyana cewa za a gurfanar da shugabannin ‘yan bindiga 19 tare da bayar da ladan naira miliyan 5 ga duk wanda ya fallasa ‘yan ta’adda don a karfafa guiwar ‘yan Nijeriya su bayar da bayanan yadda za a kai ga kama masu laifin.

ADVERTISEMENT

Sai dai kuma a wannan lokacin ba a bayar da wata kyauta kan bayar da bayanai kan mutane 97 da aka bayyana ana nema ruwa a jallo ba, wadanda suka hada da shugaban kungiyar masu fafutukar neman kafa kasar Biafra, IPOB.

Sunaye da hotunan sun kunshi ‘yan ta’adda daga Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma da kuma masu tayar da kayar baya a Kudu maso Gabas da Arewa ta Tsakiya.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Kimanin mutane 43 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a shiyyar Arewa maso Yamma, daga cikinsu akwai Alhaji Shingi da Malindi Yakubu Boka da Dogo Gide da Halilu Sububu da Ado Aliero da Bello Turji da Dan Bokkolo da Labi Yadi da Nagala da Saidu Idris da Kachalla da Rugga da kuma Sani Gurgu.

Kazalika, an bayyana mutane 33 da ake nema ruwa a jallo a yankin Arewa maso Gabas sakamakon rikicin Boko Haram da kungiyar IS mai da’awar kafa daular musulunci a yammacin Afirka.

Wasu daga cikin ‘yan ta’addar da ake nema ruwa a jallo sun hada da Abu Zaida da Modu Sulum da Baba Data da Ahmad da Sani Teacher da Baa Sadiq da Abdul Saad da Kaka Abi da Mohammad Khalifa da Umar Tella da Abu Mutahid da Malam Mohammad da kuma Malam Tahiru Baga da kuma Uzaiya da Ali Ngule.

A halin da ake ciki dai an bayyana cewa ana zargin masu tada kayar baya 21 da kuma masu aikata laifuka a yankin Kudu maso Gabas da Arewa ta Tsakiya.

Wadanda ake tuhuma da laifin sun hada da Simon EkpaEkpa da Chika Edoziem da Egede da Zuma da ThankGod da Gentle da Flavour da Mathew da David Ndubuisi da High Chief Williams Agbor da Ebuka Nwaka da Friday Ojimka da Obiemesi Chukwudi aka Dan Chuk da David Ezekwem Chidiebube da Amobi Chinonso Okafor mai inkiyar Temple da dau sauransu.

Nijeriya
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Alamomin Kansar Mama Ta Maza

Alamomin Kansar Mama Ta Maza

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.