Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

An Yi Wa Yara 30 Fyaɗe A Sansanin Gudun Hijira Da Ke Yobe

by Tayo Adelaja
October 21, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Sabo Ahmad

Kwamitin da Shugaban Ƙasa ya kafa kan kula da ‘yan gudun hijira na Arewa-maso-gabas, ya bayyana damuwarsa bisa ƙaruwar da ake samu na yawan fyaɗe da barazanar da ‘yan gudun hijirar ke fuskanta na rayukansu da dukiyoyinsu a sansanoninsu da ke Arewa-maso-gabas.

Kwamitin ya bayar da ƙiyasin cewa, kimanin yara 30 ne aka yi wa fyaɗe a sansanonin ‘yan gudun hijira da ke jihar Yobe, a cikin watan Satumba na shekara ta 2017.

Kwamitin ya ƙara da cewa, barazanar fyaɗen ga yara da manyan mata ta ƙara ƙazanta a wannan watan da muke ciki, wanda kuma ya sa ake fargabar ƙara yaɗuwar ƙwayoyin cutar ƙanjamau a sansanonin. Mataimakin shugaban kwamitin, Alhaji Tijani Tumsa, ne ya bayyana haka lokacin da suke tattauna wa da wakilan kwamitin, ranar Alhamis ɗin da ta gabata a Abuja, wanda kuma ya nuna damuwar da Majalisar Tarayya ta yi kan wannan mummunan aiki.

Tumsa ya dangata faruwar wannan al’amari da rashin cikakken tsaron da ake fama da shi a sansanonin ‘yan gudun hijirar, saboda haka, ya ce, kwamitinsu zai haɗa kai da jami’an tsaro, wajen ganin an kawo ƙarshen wannan matsala.

“Fyaɗe mummuna abu ne, musamman da yake hanya ce ma fi sauƙi ta yaɗa ƙwayoyin cutar ƙanjamau; saboda haka, abin da muka sa a gaba shi ne, duk wanda aka kama shi da wannan laifi za a yi masa hukuncin da ya dace, cikin gaggawa.” In ji shi.

Da ake tambayarsa kan yawan mutanen da suka kama bisa zarginsu da aikata wannan mummunan hali sai ya ce, ba shi da masaniya a kan yawan mutanen da aka kama, amma dai ya tabbatar da cewa, dukkan waɗanda aka Kaman suna tsare.

Ya ce, Kwamitin nasu na ƙoƙarin koya wa ‘yan gudun hijirar sana’o’i, yadda ko bayan sun koma gida za su ci gaba da gudanar da rayuwarsu cikin walwala.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Za A Sake Fasalin Dokar Haramta Shan Giya A Kaduna

Next Post

Dalilin Da Ya Sa Na Ziyarci IBB —Goodluck

RelatedPosts

Allurar Rigakafin

An Fara Yin Allurar Riga-kafin Korona a Nijeriya

by Muhammad
20 hours ago
0

Yau Ake Sa Ran Buhari Da Osinbajo Za Su Karbi...

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
2 weeks ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Adaidaita

Yajin Aikin Adaidaita: Acaba Ta Dawo A Kano

by Muhammad
2 weeks ago
0

Ya Jefa Jama’a Cikin Tsaka Mai Wuya Yadda Aka Koma...

Next Post

Dalilin Da Ya Sa Na Ziyarci IBB —Goodluck

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version