• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

by Sulaiman
3 days ago
in Labarai
0
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishina mai wakiltar jihar Kaduna a Hukumar ƙidaya ta ƙasa, Hajiya Sa’adatu Dogon Bauchi ta kawo ziyara jihar Kaduna domin ganawa da shugabannin Ƙananan Hukumomin jihar 23, tare da masu ruwa da tsaki, a shirin Hukumar na wayar da kan jama’a game da ƙidayar da ke tafe.

 

A lokacin da ta ziyarci Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, Hajiya Sa’adatu ta bayar da shawara ga al’umma kan cewa su fito ƙwan su da ƙarƙwata, su tabbatar da an ƙidaya su, domin ta haka ne kawai gwamnti za ta iya wadatar da su da ababen more rayuwa.

  • Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya
  • Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

Haka kuma Kwamishiyar ta jawo hankalin jama’a game da mahimmacin yin rajisista don karbar shaidar yin aure, haihuwa, saki, mutuwa da dai sauran su, wanda ake bayarwa a ofishin Hukumar a duk jihohin ƙasar nan.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

Hajiya Sa’ah ta kuma bayyana cewa ita wannan ƙidaya da yin rajistar haihuwa, aure da sauran su, abubuwa ne masu muhimmanci da za su taimaka wa gwamnati ta san yawan su, ta yadda za su sami nasarar ci gaba da lasar romon Dimokraɗiyya mai yawa, musamman a bangaren ilmi, lafiya da dai sauran abubuwan more rayuwa.

 

Daga nan ne ta jinjina wa Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani da cewar jihar Kaduna ce jiha ta farko da gwamnan ta ya yi yunƙurin gabatar da wayar da kan al’ummar sa game da muhimmancin ƙidaya, kuma lallai yana bayar da cikakken goyon bayan sa a kan haka, inda ya ɗauki nauyin hakan a dukkan Ƙananan Hukumomin jihar.

 

A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, Malam Jamilu Abubakar Albani (ALGON), wanda ya samu wakilcin mataimakin sa, ya bayyana cewa su a shirye suke su bayar da dukkan goyon bayan da ake nema.

 

Ya ce, su tun a baya sun fara wayar ma al’ummar Ƙaramar Hukumar su kai game da manufa da muhimmancin shirin ƙidayar a gare su. Sun shiga lungu da saƙo don wayar ma da al’ummar su kai game da shirin ƙidayar da ke tunkarowa, wanda zai gudana nan ba da jimawa ba.

 

Ɗaya daga cikin Malaman addinai da suka halarci taron ya tabbatar da ƙidayar al’umma a cikin tsarin addinin musulunci, domin shi ne yake bada damar sanin tsatson dukkan ɗan adam da kuma tabbatar da rayuwa cikin tsari.

 

Shi ma a nasa jawabin, wani Shugaba a addinin kirista ya nuna farin cikin sa, sannan kuma nuna yadda zasu wayar ma da mabiyan su kai game da ƙidayar. Ya kuma ƙara da ceawar a koyaushe hukumar ƙidayar suka shirya, su ma a shirye suke wajen ganin an cimma gaci.

 

A looacin da tawagar Kwamishiyar ta isa Ƙaramar Hukumar Soba, Shygaban Ƙaramar Hukumar, Hon. Muhammad Shehu Lawal Molash, ya bayyana jin daɗin sa da wannan shiri na ƙidaya, inda ya nuna cewa za su bayar da duk gudumawa da haɗin kan da ake nema don samun nasarar aikin.

 

Shi kuwa Sarki Haladu, jan hankalin matasa ya yi da su kauce ma duk wata hayaniya, su zama masu natsuwa tun a yanzu wajen wayar ma da al’umma kai har zuwa kammala shirin.

 

Ya zuwa haɗa wannan rahoton dai, Kwamishiniya Hajiya Sa’adatu Dogon Bauchi tana ci gaba da zagawa zuwa sauran Ƙananan Hukumomin jihar don ƙara wayar da kan jama’a game da muhimmancin wannan ƙidaya da ke tafe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

Next Post

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

2 hours ago
Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya
Labarai

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

2 hours ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

4 hours ago
An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya
Manyan Labarai

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

5 hours ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

8 hours ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

September 10, 2025
“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

September 10, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

September 10, 2025
Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

September 10, 2025
Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

September 10, 2025
Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

September 10, 2025
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

September 10, 2025
Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

September 10, 2025
An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

September 10, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.