ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Ji Dadin Abin Da Ya Faru Da Tawagar ‘Super Eagles’ A Libya Ba -Patrice Motsepe

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Super Eagles

Shugaban hukumar kwallon kafar Afirika (CAF) Patrice Motsepe a karon farko ya yi magana game da yanayin da tawagar kwallon kafar Nijeriya ta tsinci kan ta a Libya bayan zuwa buga wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka (AFCON).

Patrice Motsepe ya bayyana haka ne a wata ganawa da ya yi da manema labarai inda ya yi Allah wadai da halin da Super Eagles ta Nijeriya ta shiga a filin tashi da saukar jiragen sama na Libya gabanin wasan neman gurbin shiga gasar AFCON 2025, Motsepe ya yi Allah wadai da lamarin amma ya dage cewa ba zai yi magana kan lamarin ba har sai hukumar ta yanke shawara ta karshe.

  • Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (3)
  • Isra’ila Ta Kai Wa Iran; Saudiyya Ta Yi Jawabi

“Ya kamata mu kasance masu hakuri a kowane lokaci amma dai yanzu ba zan ce komai ba har sai lokacin da hukumar CAF ta kammala cikakken bincike akan abinda ya faru in ji shi,amma ina so in jaddada cewa wannan wani abu ne da ba za mu lamunta ba, kuma za a dauki matakin da ya dace.

ADVERTISEMENT

Na ji labarai da dama a kan abubuwan da suke faruwa a lokacin da wata kasa ta ziyarci wata kasar domin buga kwallo a nan Afirika, har ma na ji wani lokaci ana neman su bayar da takardun shaidarsu ta zama ‘yan kasa, sannan a lokacin cutar Korona sai a dubi mutum 10 da suka fi kwarewa a wasa ace suna dauke da cutar Korona da sauran korafe korafe wadanda ba za mu yarda hakan ta ci gaba da faruwa ba.

Ya ci gaba da cewa a tunanina dukkan wadannan abubuwan su na faruwa sakamakon rashin daukar wani mataki a kan masu aikata hakan,to ku sani cewa zamu gabatar da wasu tsauraran dokoki da za su taimaka wajen gyara harkar kwallon kafa a nahiyar Afirika in ji Motsepe.

LABARAI MASU NASABA

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

Tun da farko dai an shirya Nijeriya za ta kara da Libya a wasan zagaye na biyu a Talatar makon jiya ranar 15 ga watan Oktoba, 2024, amma hakan bai yiwu ba sakamakon janyewa daga wasan da Nijeriya ta yi bayan shafe awanni 20 a filin jirgi ba tare da samun kulawa daga hukumomin kasar Libya ba.

Super Eagles
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
  • Abba Ibrahim Wada
    LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 
  • Abba Ibrahim Wada
    An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

MASU ALAKA

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
Wasanni

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
Wasanni

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa
Wasanni

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Next Post
Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?

Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

July 10, 2026
Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

July 10, 2026
Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.