• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Fara Rabon Takin CBN Kyauta, Sai Dai Masana Sun Ba Da Shawara

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Za A Fara Rabon Takin CBN Kyauta, Sai Dai Masana Sun Ba Da Shawara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci ta Tarayya, ta shirya tsaf; domin fara rabon buhunan takin zamani miliyan 2.15, wanda Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya ba ta kauta.

Wasu masana a fannin aikin noma a kasar nan; sun bayar da shawarar cewa, duba da yadda aka fara samun ruwan sama a wasu sassan yankunan kasar nan, ya kamata a fara raba wa manoma takin a kan lokaci, musamman domin samar da wadataccen abinci.

  • Sin Ta Bukaci Philippines Da Ta Dakatar Da Tada Zaune Tsaye A Yankin Tekun Kudancin Sin
  • Ziyarar Xi Jinping A Turai Ta Fitar Da Muryar Kiyaye Zaman Lafiya Da Yin Hadin Gwiwa

Sai dai, wata majiya a ma’aikatar ta bayyana cewa, an samu jinkirin rabar da takin zamanin ne; sakamakon gudanar da binciken da aka yi na zargin cewa, takin ya lalace.

A cewar majiyar, “Babban Bankin CBN, ba wani sabon takin zamanin zai sayo ba, sauran wanda Tsohon Gwamnan Babban Bankin, Godwin Emefiele ya gaza rabawa ne a karkashin shirin  aikin noma na babban bankin, wato ‘Anchor Borrower Programme’.”

Har ila yau, majiyar ta kara da cewa; wannan taki, bankin CBN ne ya mika wa ma’aiktar aikin noma, amma akwai wasu abubuwa da ma’aikatar ke bukatar tantacewa kafin ta fara rabar da takin.

Haka kazalika, akwai wani zargi da ake yi na cewa, tuni takin ya jima da lalacewa.

Koda-yake, an kuma ruwaito cewa; Daraktan sashen kula da ayyukan samar da kayan aiki noma na ma’aikatar, Abana Waziri Abba, ya karyata batun zargin lalacewar takin zamanin.

Sai dai kuma, ya aminta da cewa; sashen ya dauki samfurin takin, don gudanar da gwaji a dakunan gwaje-gwajen da ake da su a Jihar Kaduna da Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya da kuma Jami’ar  Bayero da ke Kano, don tabbatar da ingancinsa; domin wannan sashe ne ke da alhakin tabbatar da ingancin kowane irin taki a fadin kasar nan.

A cewarsa, sakamakon binciken ya nuna cewa, takin na da inganci; sannan kuma za a iya sayar wa da manoma, inda ya sanar da cewa, sai dai kawai wasu ‘yan matsaloli da ba za a rasa ba a kan takin.

Sai dai, bai yi bayani dalla-dalla kan yadda za a yi rabon takin ga manoman da ke fadin Nijeriya ba.

Kazalika, yawan takin ya kai kimanin buhu miliyan 2.15, sannan kowane nauyin buhu daya ya kai nauyin kilo 50.

Sa’annan, nau’in takin ya hada da NPK tan 27,250; 20-10-10 da wani tan 27,110.00 na NPK 27-13-13 da tan 18,904.55 na NPK 15-15-15  378,091 da tan  31,772.18 na nau’in UREA 635,444 da kuma tan 2,500 na nau’in  SSP 50,000.

Jimillar wadannan nau’ikan baki-daya ya kai yawan buhu 2,150,735, wadanda awonsu ya kai kimanin tan 107,536.73.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNNomaTaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Kira Da Aiwatar Da Matakan Samar Da Ilimi Mai Inganci A Nahiyar Afirka

Next Post

Tsohon Firaministan Faransa: Duniya Na Hasashen Kyakkyawar Makoma Ga Kasar Sin

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

7 days ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

7 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
Tsohon Firaministan Faransa: Duniya Na Hasashen Kyakkyawar Makoma Ga Kasar Sin

Tsohon Firaministan Faransa: Duniya Na Hasashen Kyakkyawar Makoma Ga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.