• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba cocin nan na Kenya da ake zargi da laifin tilasta wa mabiyansa azumin mutuwa don haduwa da Yesu Almasihu ya sake bayyana a gaban kotu ranar Larabar nan, bayan gurfana da ya yi a ranar Talata.

Hukumomi na gudanar da bincike kan yiwuwar cewa an yi amfani da sassan jikin mutanen da suka mutun.

  • Zaɓen Gwamna: INEC Ta Fitar Da Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓuɓɓukan Cike Gurbi Na Jihohin Kogi, Bayelsa Da Imo
  • Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

Binciken ‘yan sanda ya nuna yadda aka gano karin wasu gawawwakin da aka cire sassan jikinsu.

 Wannan ya sa ake ganin da alama an yi amfani da sassan jikin gawawwakin mabiyan na Cocin Good News International, da aka gano a dajin Shakahola na kasar ta Kenya.

Kusan a kullum aka ci gaba da binciken da ake yi tun da aka fara gano wannan al’amari a tsakiyar watan Afrilu sai an samu karin gawawwaki, inda yanzu aka samu 133.

Labarai Masu Nasaba

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

Ana zargin shugaban cocin Good News International, Pastor Paul Mackenzie mai shekara 50 da sanya mabiyansa azumi har su mutu, ko su kashe kansu a dalilin hudubar da ya yi musu cewa duniya za ta tashi ranar 15 ga watan Afirilun da ya gabata.

 Ya gaya musu cewa idan suka mutu za su shiga aljanna inda za su hadu da Yesu Almasihu.

Mutanen da aka gano sun mutu ko dai a dalilin azumin da ya kai su ga yunwa har suka mutu ko kuma an shake su ko kuma sun mutu a dalilin buga musu wani abu.

Kungiyar agaji ta Red Cross a kasar ta Kenya ta ce har yanzu akwai mutane 566 da ba a san inda suke ba.

Yayin da mai binciken gawawwaki na gwamnatin kasar ya ce ko dai gawawwakin sarai suke ba a cire wani sashe na jikinsu ba, ko kuma wasu sassan nasu sun fara rubewa, binciken ‘yan sanda ya nuna sabanin hakan.

An gano cewa an ciccire sassan jikin wasu, wanda hakan ke nuna yuwuwar an yi amfani da sassan jikin mutanen.

Ministan tsaro na Kenya ya ce wannan lamari wani mugun laifi ne da aka tsar shi sosai, kuma aikin tono gawawwakin zai dauki lokaci fiye da yadda aka yi tsammani.

A halin da ake ciki kuma an rantsar da wata hukumar bincike ta musamman a babban birnin kasar Nairobi, da kuma wani kwamiti na musamman da na sanya ido a kan harkokin addini domin su gudanar da bincike a kan lamarin.

Masu binciken laifuka a Kenya sun tono karin gawarwaki 21 bayan kaddamar da sabon bincike kan lamarin.

Ministan cikin gida na Kenya Kithure Kindiki ya ce su na binciken ko an yanke gabobin wasu gawawwakin don safarar gabobi.

An dakatar da tono gawawwakin saboda rashin kyawun yanayi a dajin na Shakahola.

An fara tuhumar faston tare da wasu mutanen 14 kan laifukan ta’addanci da dora mutane kan tsattsaurar akida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaCociKotuMabiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

Next Post

Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi

Related

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

6 days ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

6 days ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

6 days ago
An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

1 month ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

1 month ago
Next Post
Sojoji 2 Da Farar Hula 1 Sun Mutum A Wani Hatsarin Mota A Legas

Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

August 22, 2025
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.