• English
  • Business News
Wednesday, May 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba cocin nan na Kenya da ake zargi da laifin tilasta wa mabiyansa azumin mutuwa don haduwa da Yesu Almasihu ya sake bayyana a gaban kotu ranar Larabar nan, bayan gurfana da ya yi a ranar Talata.

Hukumomi na gudanar da bincike kan yiwuwar cewa an yi amfani da sassan jikin mutanen da suka mutun.

  • Zaɓen Gwamna: INEC Ta Fitar Da Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓuɓɓukan Cike Gurbi Na Jihohin Kogi, Bayelsa Da Imo
  • Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

Binciken ‘yan sanda ya nuna yadda aka gano karin wasu gawawwakin da aka cire sassan jikinsu.

 Wannan ya sa ake ganin da alama an yi amfani da sassan jikin gawawwakin mabiyan na Cocin Good News International, da aka gano a dajin Shakahola na kasar ta Kenya.

Kusan a kullum aka ci gaba da binciken da ake yi tun da aka fara gano wannan al’amari a tsakiyar watan Afrilu sai an samu karin gawawwaki, inda yanzu aka samu 133.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Ana zargin shugaban cocin Good News International, Pastor Paul Mackenzie mai shekara 50 da sanya mabiyansa azumi har su mutu, ko su kashe kansu a dalilin hudubar da ya yi musu cewa duniya za ta tashi ranar 15 ga watan Afirilun da ya gabata.

 Ya gaya musu cewa idan suka mutu za su shiga aljanna inda za su hadu da Yesu Almasihu.

Mutanen da aka gano sun mutu ko dai a dalilin azumin da ya kai su ga yunwa har suka mutu ko kuma an shake su ko kuma sun mutu a dalilin buga musu wani abu.

Kungiyar agaji ta Red Cross a kasar ta Kenya ta ce har yanzu akwai mutane 566 da ba a san inda suke ba.

Yayin da mai binciken gawawwaki na gwamnatin kasar ya ce ko dai gawawwakin sarai suke ba a cire wani sashe na jikinsu ba, ko kuma wasu sassan nasu sun fara rubewa, binciken ‘yan sanda ya nuna sabanin hakan.

An gano cewa an ciccire sassan jikin wasu, wanda hakan ke nuna yuwuwar an yi amfani da sassan jikin mutanen.

Ministan tsaro na Kenya ya ce wannan lamari wani mugun laifi ne da aka tsar shi sosai, kuma aikin tono gawawwakin zai dauki lokaci fiye da yadda aka yi tsammani.

A halin da ake ciki kuma an rantsar da wata hukumar bincike ta musamman a babban birnin kasar Nairobi, da kuma wani kwamiti na musamman da na sanya ido a kan harkokin addini domin su gudanar da bincike a kan lamarin.

Masu binciken laifuka a Kenya sun tono karin gawarwaki 21 bayan kaddamar da sabon bincike kan lamarin.

Ministan cikin gida na Kenya Kithure Kindiki ya ce su na binciken ko an yanke gabobin wasu gawawwakin don safarar gabobi.

An dakatar da tono gawawwakin saboda rashin kyawun yanayi a dajin na Shakahola.

An fara tuhumar faston tare da wasu mutanen 14 kan laifukan ta’addanci da dora mutane kan tsattsaurar akida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaCociKotuMabiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

Next Post

Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

1 month ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

3 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Sojoji 2 Da Farar Hula 1 Sun Mutum A Wani Hatsarin Mota A Legas

Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

May 20, 2025
Xi Ya Jaddada Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaba Mai Inganci A Kasar Yayin Ziyararsa A Henan 

Xi Ya Jaddada Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaba Mai Inganci A Kasar Yayin Ziyararsa A Henan 

May 20, 2025
EFCC Ta Miƙa Gidaje 750 Na Emefiele Da Ta Ƙwace Ga Ministan Gidaje

EFCC Ta Miƙa Gidaje 750 Na Emefiele Da Ta Ƙwace Ga Ministan Gidaje

May 20, 2025
Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

May 20, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin SCO Na 2025

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin SCO Na 2025

May 20, 2025
Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

May 20, 2025
Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

May 20, 2025
Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola

Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola

May 20, 2025
Ana Zargin ‘Yansanda Da Keta Haddin Dan Jarida A Kano

‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

May 20, 2025
An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

May 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.