Hukumar Hasashen Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta ce daga ranar Juma’a zuwa Lahadi za a yi ruwan sama mai yawa a wasu jihohi na ƙasar nan.
Jihohin da za a fi samun ruwan sama su ne: Kano, Katsina, Sakkwato,Kebbi, Zamfara, Kaduna, Jigawa, Borno, Yobe da Taraba.
A waɗannan wurare ruwan zai zo da iska mai ƙarfi.
A Arewa ta Tsakiya kuwa, NiMet ta ce za a samu ruwan sama kaɗan a jihohin Nasarawa, Benuwe, Kogi, Kwara, Neja, Filato da kuma Abuja.
A yankin Kudu kuma, za a samu ruwan sama kaɗan tare da yanayin zafi a jihohin Oyo, Osun, Ekiti, Ondo, Edo, Enugu, Imo, Abiya, Anambra, Delta, Ribas, Bayelsa, Cross Ribas da kuma Akwa Ibom.
NiMet ta gargaɗi mutane su yi hattara a lokacin ruwan sama, musamman masu tuƙin mota, sannan a cire na’urorin lantarki daga wuta, kuma a guji zama ƙarƙashin manyan bishiyoyi.
Haka kuma, ta shawarci manoma su guji amfani da taki da maganin ƙwari kafin ruwa ya sauka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp