• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda

by Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi, ta ce, ta sake shirin samar da isashshen tsaro domin gudanar da zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi ba tare da tangarda ba a fadin jihar.

Kwamishinan ‘yansandan Jihar, CP Ahmed Magaji-Kontagora ne ya bayyana hakan yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Birnin Kebbi a ranar Juma’a.

  • Birtaniya Da Faransa Za Su Tattauna Kan Makomar Bakin Haure
  • Ban Damu Da Hadakar PDP Da Sauran Jam’iyyu Ba -Uba Sani

Wakilinmu ya ruwaito cewa taron wanda hukumar ta shirya domin hada kan masu ruwa da tsaki a harkar siyasa ya samu wakilai daga jam’iyyun siyasa daban-daban na jihar da kuma wakilan Sarakunan gargajiya na jihar.

CP ya ce, makasudin taron shi ne duba yadda al’ummar jihar suka gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da kuma tsara hanyoyin da za a bi wajen tabbatar da zaben gwamna cikin lumana da nasara da kuma rashin cikas.

“Ba mun taru nan ne don yin fada ba amma mun taru ne don yin mu’amala da tunani kan yadda za a gudanar da zabe cikin lumana, ba tare da cikas ba, cikin nasara da kuma karbuwa a zaben gwamna mai zuwa,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

A yayin da yake yaba wa al’ummar jihar Kebbi bisa yadda suka fito domin gudanar da aikinsu cikin tsari a lokacin zaben da ya gabata, Magaji-Kontagora ya yi kira gare su da su ci gaba da gudanar da ayyukansu, su ba su goyon baya da ba jami’an tsaro hadin kai don ba su damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Ya kuma bukaci iyaye da masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa da su ja kunnen ‘ya’yansu maza da mata da masu goyon bayan jam’iyya kan aikata aikin ta ta’adanci, rashin da’a da duk wani abu da zai iya haifar da rashin zaman lafiya kafin zabe da kuma bayan zabe.

A karshe kwamishinan ‘yansandan Magaji-Kontagora ya yi kira ga ‘yan jarida da su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ba tare da karkata a wani bangare ba, inda ya bukace su da su guji duk wani nau’i na labarun ban sha’awa don a samar da hanyar zaman lafiya a kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Umarnin Bincike Kan Hatsarin Jirgin Kasa Da Mota A Legas

'Yansanda Sun Ce Cafke Direban Bas Kan Hadarin Jirgin Kasa A Legas

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.