• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi, ta ce, ta sake shirin samar da isashshen tsaro domin gudanar da zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi ba tare da tangarda ba a fadin jihar.

Kwamishinan ‘yansandan Jihar, CP Ahmed Magaji-Kontagora ne ya bayyana hakan yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Birnin Kebbi a ranar Juma’a.

  • Birtaniya Da Faransa Za Su Tattauna Kan Makomar Bakin Haure
  • Ban Damu Da Hadakar PDP Da Sauran Jam’iyyu Ba -Uba Sani

Wakilinmu ya ruwaito cewa taron wanda hukumar ta shirya domin hada kan masu ruwa da tsaki a harkar siyasa ya samu wakilai daga jam’iyyun siyasa daban-daban na jihar da kuma wakilan Sarakunan gargajiya na jihar.

CP ya ce, makasudin taron shi ne duba yadda al’ummar jihar suka gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da kuma tsara hanyoyin da za a bi wajen tabbatar da zaben gwamna cikin lumana da nasara da kuma rashin cikas.

“Ba mun taru nan ne don yin fada ba amma mun taru ne don yin mu’amala da tunani kan yadda za a gudanar da zabe cikin lumana, ba tare da cikas ba, cikin nasara da kuma karbuwa a zaben gwamna mai zuwa,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

A yayin da yake yaba wa al’ummar jihar Kebbi bisa yadda suka fito domin gudanar da aikinsu cikin tsari a lokacin zaben da ya gabata, Magaji-Kontagora ya yi kira gare su da su ci gaba da gudanar da ayyukansu, su ba su goyon baya da ba jami’an tsaro hadin kai don ba su damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Ya kuma bukaci iyaye da masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa da su ja kunnen ‘ya’yansu maza da mata da masu goyon bayan jam’iyya kan aikata aikin ta ta’adanci, rashin da’a da duk wani abu da zai iya haifar da rashin zaman lafiya kafin zabe da kuma bayan zabe.

A karshe kwamishinan ‘yansandan Magaji-Kontagora ya yi kira ga ‘yan jarida da su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ba tare da karkata a wani bangare ba, inda ya bukace su da su guji duk wani nau’i na labarun ban sha’awa don a samar da hanyar zaman lafiya a kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaKebbiTsaroZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Shugabannin Kasashen Duniya Sun Taya Xi Jinping Murnar Ci Gaba Da Kasancewa Shugaban Kasar Sin

Next Post

‘Yansanda Sun Ce Cafke Direban Bas Kan Hadarin Jirgin Kasa A Legas

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

4 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

6 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

7 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

8 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

9 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Umarnin Bincike Kan Hatsarin Jirgin Kasa Da Mota A Legas

'Yansanda Sun Ce Cafke Direban Bas Kan Hadarin Jirgin Kasa A Legas

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.