ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda

by Umar Faruk
4 years ago
Kebbi

Rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi, ta ce, ta sake shirin samar da isashshen tsaro domin gudanar da zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi ba tare da tangarda ba a fadin jihar.

Kwamishinan ‘yansandan Jihar, CP Ahmed Magaji-Kontagora ne ya bayyana hakan yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Birnin Kebbi a ranar Juma’a.

  • Birtaniya Da Faransa Za Su Tattauna Kan Makomar Bakin Haure
  • Ban Damu Da Hadakar PDP Da Sauran Jam’iyyu Ba -Uba Sani

Wakilinmu ya ruwaito cewa taron wanda hukumar ta shirya domin hada kan masu ruwa da tsaki a harkar siyasa ya samu wakilai daga jam’iyyun siyasa daban-daban na jihar da kuma wakilan Sarakunan gargajiya na jihar.

ADVERTISEMENT

CP ya ce, makasudin taron shi ne duba yadda al’ummar jihar suka gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da kuma tsara hanyoyin da za a bi wajen tabbatar da zaben gwamna cikin lumana da nasara da kuma rashin cikas.

“Ba mun taru nan ne don yin fada ba amma mun taru ne don yin mu’amala da tunani kan yadda za a gudanar da zabe cikin lumana, ba tare da cikas ba, cikin nasara da kuma karbuwa a zaben gwamna mai zuwa,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A yayin da yake yaba wa al’ummar jihar Kebbi bisa yadda suka fito domin gudanar da aikinsu cikin tsari a lokacin zaben da ya gabata, Magaji-Kontagora ya yi kira gare su da su ci gaba da gudanar da ayyukansu, su ba su goyon baya da ba jami’an tsaro hadin kai don ba su damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Ya kuma bukaci iyaye da masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa da su ja kunnen ‘ya’yansu maza da mata da masu goyon bayan jam’iyya kan aikata aikin ta ta’adanci, rashin da’a da duk wani abu da zai iya haifar da rashin zaman lafiya kafin zabe da kuma bayan zabe.

A karshe kwamishinan ‘yansandan Magaji-Kontagora ya yi kira ga ‘yan jarida da su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ba tare da karkata a wani bangare ba, inda ya bukace su da su guji duk wani nau’i na labarun ban sha’awa don a samar da hanyar zaman lafiya a kasa.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Umarnin Bincike Kan Hatsarin Jirgin Kasa Da Mota A Legas

'Yansanda Sun Ce Cafke Direban Bas Kan Hadarin Jirgin Kasa A Legas

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.