• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar An Zakulo Makasan Sheikh Albani Kuri – Gwamnan Gombe 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Za Mu Tabbatar An Zakulo Makasan Sheikh Albani Kuri – Gwamnan Gombe 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya sha alwashin cewa, za su bayar da dukkanin gudunmawa da goyon baya ga jami’an tsaro domin tabbatar da zakulo da kamo makasan babban malamin addinin Musluncin nan, Sheikh Ibrahim H. Musa Albani Kuri da ke jihar Gombe. 

 

Idan za ku tuna dai LEADERSHIP Hausa ta bada labarin cewa wasu ‘yan bindiga dadi sun haura gidan Sheikh Albani Kuri da ke Tabra, anguwar dake gefen hanyar ratse ta Bypass Gombe tare da yi masa kisan gilla a daren ranar Laraba.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sheikh Albanin Kuri A Gombe

Gwamnan ya nuna matukar kadu da jin labarin rasuwar tare da shan alwashin daukan kwararan matakai na kamo makasan domin su fuskanci Shari’a.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Gwamna Inuwa wanda ya halarci sallar jana’izar marigayin a masallacin Izala da ke Bolari Gombe, ya yi tir da kakkausar murya kan wannan mummunan aika-aikar da ya ce ya girgiza al’amuran tsaro da zaman lafiya da ake da shi a Jihar Gombe.

Sheikh Albani Kuri

“Mu na tabbatarwa al’ummar Jihar Gombe cewa gwamnati a tsaye take tsayin daka wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiyan al’ummarta, za mu ci gaba da daukan kwararan matakai ta hanyar amfani da karfin jami’an tsaronmu don kawar da masu aikata laifuka a duk inda suke a fadin jihar nan, tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan danyen aikin a gaban kuliya don magance sake afkuwar irin haka.

 

“Wannan abu da ya faru ga Sheikh Ibrahim Albani Kuri zai zame mana hannunka mai sanda, cewa wajibi ne mu ci gaba da yin taka tsantsan da tsayin daka wajen samar da al’umma mai ci gaba, inda kowa zai iya rayuwa cikin aminci ba tare da tsoro ba”.

 

Ya kuma bukaci al’ummar jihar su ci gaba da hada kai cikin taimakekeniyar juna, tare da dabbaƙa dabi’un tausayawa da hadin kai wadda shugabanninmu na addinin suke ta kira a kai ba dare ba rana.

 

“Jama’ar jihar nan baki daya su na cikin alhinin kisan wannan malami, wadda koyarwarsa ta yi tasiri ga rayuwar al’ummar Musulmi da dama.”

 

Gwamna Inuwa ya ce marigayi Sheikh Ibrahim ya kasance mabubbugar ilimi, wadda ke karfafa fahimta da hadin kai, wanda koyarwarsa ta yi tasiri wajen ƙarfafa haɗin kan jama’a. Ya ce kowa zai ji zafin rashin wannan malami matuƙa, kuma abin da ya bari zai ci gaba da zaburar da al’umma a kullum.

 

Gwamnan a madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, da kuma kungiyar Izala da dokacin al’ummar musulmi bisa wannan rashi na bakin ciki. Ya yi addu’ar Allah Ta’ala ya saka masa da Aljannar Firdausi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Albanin KuriGombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ci Gaban Kasar Sin Abun Koyi Ne Ga Kasashen Afrika

Next Post

An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

5 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

7 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

8 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

12 hours ago
Sheikh Albani Kuri
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

13 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

14 hours ago
Next Post
An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.