• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar An Zakulo Makasan Sheikh Albani Kuri – Gwamnan Gombe 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Za Mu Tabbatar An Zakulo Makasan Sheikh Albani Kuri – Gwamnan Gombe 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya sha alwashin cewa, za su bayar da dukkanin gudunmawa da goyon baya ga jami’an tsaro domin tabbatar da zakulo da kamo makasan babban malamin addinin Musluncin nan, Sheikh Ibrahim H. Musa Albani Kuri da ke jihar Gombe. 

 

Idan za ku tuna dai LEADERSHIP Hausa ta bada labarin cewa wasu ‘yan bindiga dadi sun haura gidan Sheikh Albani Kuri da ke Tabra, anguwar dake gefen hanyar ratse ta Bypass Gombe tare da yi masa kisan gilla a daren ranar Laraba.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sheikh Albanin Kuri A Gombe

Gwamnan ya nuna matukar kadu da jin labarin rasuwar tare da shan alwashin daukan kwararan matakai na kamo makasan domin su fuskanci Shari’a.

 

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Gwamna Inuwa wanda ya halarci sallar jana’izar marigayin a masallacin Izala da ke Bolari Gombe, ya yi tir da kakkausar murya kan wannan mummunan aika-aikar da ya ce ya girgiza al’amuran tsaro da zaman lafiya da ake da shi a Jihar Gombe.

Sheikh Albani Kuri

“Mu na tabbatarwa al’ummar Jihar Gombe cewa gwamnati a tsaye take tsayin daka wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiyan al’ummarta, za mu ci gaba da daukan kwararan matakai ta hanyar amfani da karfin jami’an tsaronmu don kawar da masu aikata laifuka a duk inda suke a fadin jihar nan, tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan danyen aikin a gaban kuliya don magance sake afkuwar irin haka.

 

“Wannan abu da ya faru ga Sheikh Ibrahim Albani Kuri zai zame mana hannunka mai sanda, cewa wajibi ne mu ci gaba da yin taka tsantsan da tsayin daka wajen samar da al’umma mai ci gaba, inda kowa zai iya rayuwa cikin aminci ba tare da tsoro ba”.

 

Ya kuma bukaci al’ummar jihar su ci gaba da hada kai cikin taimakekeniyar juna, tare da dabbaƙa dabi’un tausayawa da hadin kai wadda shugabanninmu na addinin suke ta kira a kai ba dare ba rana.

 

“Jama’ar jihar nan baki daya su na cikin alhinin kisan wannan malami, wadda koyarwarsa ta yi tasiri ga rayuwar al’ummar Musulmi da dama.”

 

Gwamna Inuwa ya ce marigayi Sheikh Ibrahim ya kasance mabubbugar ilimi, wadda ke karfafa fahimta da hadin kai, wanda koyarwarsa ta yi tasiri wajen ƙarfafa haɗin kan jama’a. Ya ce kowa zai ji zafin rashin wannan malami matuƙa, kuma abin da ya bari zai ci gaba da zaburar da al’umma a kullum.

 

Gwamnan a madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, da kuma kungiyar Izala da dokacin al’ummar musulmi bisa wannan rashi na bakin ciki. Ya yi addu’ar Allah Ta’ala ya saka masa da Aljannar Firdausi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Albanin KuriGombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ci Gaban Kasar Sin Abun Koyi Ne Ga Kasashen Afrika

Next Post

An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

3 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

3 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

9 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

11 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

11 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

14 hours ago
Next Post
An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.