ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar An Zakulo Makasan Sheikh Albani Kuri – Gwamnan Gombe 

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Sheikh Albani Kuri

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya sha alwashin cewa, za su bayar da dukkanin gudunmawa da goyon baya ga jami’an tsaro domin tabbatar da zakulo da kamo makasan babban malamin addinin Musluncin nan, Sheikh Ibrahim H. Musa Albani Kuri da ke jihar Gombe. 

 

Idan za ku tuna dai LEADERSHIP Hausa ta bada labarin cewa wasu ‘yan bindiga dadi sun haura gidan Sheikh Albani Kuri da ke Tabra, anguwar dake gefen hanyar ratse ta Bypass Gombe tare da yi masa kisan gilla a daren ranar Laraba.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sheikh Albanin Kuri A Gombe

Gwamnan ya nuna matukar kadu da jin labarin rasuwar tare da shan alwashin daukan kwararan matakai na kamo makasan domin su fuskanci Shari’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Gwamna Inuwa wanda ya halarci sallar jana’izar marigayin a masallacin Izala da ke Bolari Gombe, ya yi tir da kakkausar murya kan wannan mummunan aika-aikar da ya ce ya girgiza al’amuran tsaro da zaman lafiya da ake da shi a Jihar Gombe.

Sheikh Albani Kuri

“Mu na tabbatarwa al’ummar Jihar Gombe cewa gwamnati a tsaye take tsayin daka wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiyan al’ummarta, za mu ci gaba da daukan kwararan matakai ta hanyar amfani da karfin jami’an tsaronmu don kawar da masu aikata laifuka a duk inda suke a fadin jihar nan, tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan danyen aikin a gaban kuliya don magance sake afkuwar irin haka.

 

“Wannan abu da ya faru ga Sheikh Ibrahim Albani Kuri zai zame mana hannunka mai sanda, cewa wajibi ne mu ci gaba da yin taka tsantsan da tsayin daka wajen samar da al’umma mai ci gaba, inda kowa zai iya rayuwa cikin aminci ba tare da tsoro ba”.

 

Ya kuma bukaci al’ummar jihar su ci gaba da hada kai cikin taimakekeniyar juna, tare da dabbaƙa dabi’un tausayawa da hadin kai wadda shugabanninmu na addinin suke ta kira a kai ba dare ba rana.

 

“Jama’ar jihar nan baki daya su na cikin alhinin kisan wannan malami, wadda koyarwarsa ta yi tasiri ga rayuwar al’ummar Musulmi da dama.”

 

Gwamna Inuwa ya ce marigayi Sheikh Ibrahim ya kasance mabubbugar ilimi, wadda ke karfafa fahimta da hadin kai, wanda koyarwarsa ta yi tasiri wajen ƙarfafa haɗin kan jama’a. Ya ce kowa zai ji zafin rashin wannan malami matuƙa, kuma abin da ya bari zai ci gaba da zaburar da al’umma a kullum.

 

Gwamnan a madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, da kuma kungiyar Izala da dokacin al’ummar musulmi bisa wannan rashi na bakin ciki. Ya yi addu’ar Allah Ta’ala ya saka masa da Aljannar Firdausi.

Sheikh Albani Kuri
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.