ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar An Zakulo Makasan Sheikh Albani Kuri – Gwamnan Gombe 

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Sheikh Albani Kuri

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya sha alwashin cewa, za su bayar da dukkanin gudunmawa da goyon baya ga jami’an tsaro domin tabbatar da zakulo da kamo makasan babban malamin addinin Musluncin nan, Sheikh Ibrahim H. Musa Albani Kuri da ke jihar Gombe. 

 

Idan za ku tuna dai LEADERSHIP Hausa ta bada labarin cewa wasu ‘yan bindiga dadi sun haura gidan Sheikh Albani Kuri da ke Tabra, anguwar dake gefen hanyar ratse ta Bypass Gombe tare da yi masa kisan gilla a daren ranar Laraba.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sheikh Albanin Kuri A Gombe

Gwamnan ya nuna matukar kadu da jin labarin rasuwar tare da shan alwashin daukan kwararan matakai na kamo makasan domin su fuskanci Shari’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Gwamna Inuwa wanda ya halarci sallar jana’izar marigayin a masallacin Izala da ke Bolari Gombe, ya yi tir da kakkausar murya kan wannan mummunan aika-aikar da ya ce ya girgiza al’amuran tsaro da zaman lafiya da ake da shi a Jihar Gombe.

Sheikh Albani Kuri

“Mu na tabbatarwa al’ummar Jihar Gombe cewa gwamnati a tsaye take tsayin daka wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiyan al’ummarta, za mu ci gaba da daukan kwararan matakai ta hanyar amfani da karfin jami’an tsaronmu don kawar da masu aikata laifuka a duk inda suke a fadin jihar nan, tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan danyen aikin a gaban kuliya don magance sake afkuwar irin haka.

 

“Wannan abu da ya faru ga Sheikh Ibrahim Albani Kuri zai zame mana hannunka mai sanda, cewa wajibi ne mu ci gaba da yin taka tsantsan da tsayin daka wajen samar da al’umma mai ci gaba, inda kowa zai iya rayuwa cikin aminci ba tare da tsoro ba”.

 

Ya kuma bukaci al’ummar jihar su ci gaba da hada kai cikin taimakekeniyar juna, tare da dabbaƙa dabi’un tausayawa da hadin kai wadda shugabanninmu na addinin suke ta kira a kai ba dare ba rana.

 

“Jama’ar jihar nan baki daya su na cikin alhinin kisan wannan malami, wadda koyarwarsa ta yi tasiri ga rayuwar al’ummar Musulmi da dama.”

 

Gwamna Inuwa ya ce marigayi Sheikh Ibrahim ya kasance mabubbugar ilimi, wadda ke karfafa fahimta da hadin kai, wanda koyarwarsa ta yi tasiri wajen ƙarfafa haɗin kan jama’a. Ya ce kowa zai ji zafin rashin wannan malami matuƙa, kuma abin da ya bari zai ci gaba da zaburar da al’umma a kullum.

 

Gwamnan a madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, da kuma kungiyar Izala da dokacin al’ummar musulmi bisa wannan rashi na bakin ciki. Ya yi addu’ar Allah Ta’ala ya saka masa da Aljannar Firdausi.

Sheikh Albani Kuri
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.