• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabar Mataimaki: Tinubu Ya Watsa Wa Gwamnonin Arewa Maso Yamma Kasa A Ido

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
Zabar Mataimaki: Tinubu Ya Watsa Wa Gwamnonin Arewa Maso Yamma Kasa A Ido
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya zabi tsohon gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima a matsayin wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2023.

Sai dai zabin nasa ya yi fami na gyambon ciwo ga wasu gwamnoni da mabiya a arewa maso yamma.

  • 2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu
  • Ku Kara Kaimi Wajen Inganta Tsaro – Buhari Ga Shugabanni Tsaro

Tun farko a jam’iyyar APC an shiga tsilla-tsilla kan wane ne ya fi dacewa ya yi wa Tinubu takarar mataimaki, lamarin da ya kai ga dan takarar daukar Kabiru Ibrahim Masari a matsayin mataimaki na wucin gadi.

Sai dai shi ma, Masarin ya yi murabus daga mukamin nasa gabanin bayyana daukar Shettima da Tinubu ya yi.

Sai dai wannan hukunci na Tinubu bai yi wa da dama dadi ba, ganin cewar suna da yakinin gwamnonin arewa maso yamma na muhimman mutanen da zasu iya cike masa wancan gibi.

Labarai Masu Nasaba

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

Wasu magoya baya na ganin cewar gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje na iya zama mataimakin Tinubu a zaben 2023, duba da irin gudunmawar da ya ba shi.

Wasu na ganin Ganduje yayi bajinta sosai tun farkon fara tafiyar Tinubu ta nuna son yi takarar shugaban kasa, inda suke da yakinin cewar gwamnan na Kano, na da gogewa da kuma duk abin da ake bukata sama da zabin na Tinubu (Shettima).

Wasu kuma na ganin cewar gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, shi ne zabin da zai sa APC ta jijjiga jam’iyyar adawa ta PDP a babban zaben 2023.

Da fari wasu sun fara kiraye-kirayen da Tinubu ya dauki gwamnan na Kaduna, sai dai ba a san me ya faru aka haihu a ragaya ba.

A tunani irin na wadancan masu son Tinubu ya dauki El-Rufai, sun bayyana cewar gwamnan ya zama zakaran gwajin-dafi idan aka kwatanta shi da duk gwamnonin Nijeriya, wajen sanin salon shugabanci da kuma kware wajen sarrafa ayyukan ci gaba, musamman idan aka yi duba da yadda ya sauya fasalin birnin tarayya Abuja, lokacin da ya rike mukamin minista.

A wani kaulin kuwa, wasu masu sharhin siyasa na ganin Badaru Abubakar na jihar Jigawa, na iya zama mataimakin takarar Tinubu.

Wannan tunani nasu ba zai rasa nasaba da irin gudunmawar da a gwamnan na Jigawa ya bayar wajen farfado da jam’iyyar daga gargarar mutuwa a lokacin da ta ke fama da rikice-rikicen cikin gida ba.

Gwamnan na daga cikin mambobin kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar karkashin jagorancin Mai Mala Buni.

Har ila yau, suna ganin janyewa Tinubu takarar shugaban kasa da gwamnan yayi a zaben fidda-gwanin APC, wannan ma wata alama ce da ke nuni da dacewar a zabe shi.

Sai dai duk da wannan kiraye-kiraye da wasu ke yi na zabar daya daga cikin gwamnonin na arewa maso yamma bai yi tasiri ba, domin kuwa Tinubu ya kunnen uwar shegu da su.

Tsohon gwamnan na Legas, ya zabi shugaban yakin neman zabensa na takarar shugaban kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023BadaruEl-RufaiGandujeJigawaKadunakanoKashim ShettimaMataimakiTakarar Shugaban KasaTinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 18 A Zamfara, Mutane Sun Tsere Daga Gidajensu

Next Post

Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

Related

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

10 hours ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

2 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

3 days ago
Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani
Manyan Labarai

Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani

3 days ago
PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke
Siyasa

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

3 days ago
PDP Ta Ƙalubalanci Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Garki/Babura A Jigawa
Siyasa

PDP Ta Ƙalubalanci Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Garki/Babura A Jigawa

4 days ago
Next Post
Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.