ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu

by Sadiq
4 years ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya shawarci dan takarar shugaban kasa a APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da ya kula da lafiyarsa gabanin shiga zaben 2023.

Kwankwaso, wanda tsohon ministan tsaro ne kuma wanda ya mulki jihar Kano sau biyu, yayin wata hira da gidan talabijin na Arise News a ranar Lahadi, ya ce kamata ya yi Tinubu ya kula da lafiyarsa, inda ya yi gargadin cewa yakin neman zaben 2023 zai kasance da tsauri.

  • Goron Sallah: Shugaban APC Ya Yi Wa Nijeriya Addu’ar Zaman Lafiya
  • 2023: Kalubalen Tsaro Na Zama Barazana A Wasu Jihohin Arewacin Nijeriya

“Idan ka ga abokina Bola, ka ce masa ya bi a sannu, ya kula da lafiyarsa sosai… saboda ina sonsa sosai, abokina ne.

ADVERTISEMENT

“Wannan yakin neman zaben zai yi tsauri sosai, yana bukatar jajircewa sosai da dai sauransu. Ina fatan zai yi sauki domin mu ci gaba da fafutukar tabbatar da kasa daya mai karfi da wadata a Nijeriya,” in ji Kwankwaso.

Da aka tambaye shi ko Tinubu na masa barazana, Kwankwaso, wanda shi ne mataimakin kakakin majalisar wakilai a jamhuriya ta uku, ya ce Tinubu a matsayinsa a kashin kansa mutumin kirki ne amma bai san abin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC zai yi daban da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

“Damuwata kawai ita ce jam’iyyar da ya fito. Na san shi mai dabara ne, Bola Tinubu, mutumin kirki ne. Na zauna tare da shi sau da yawa ba za a iya kirgawa ba daga 1992 zuwa yau.

“Ina fatan idan gan shi zan tambaye shi me zai gaya wa ‘yan Nijeriya abin da zai yi na daban da abin da Muhammadu Buhari ke yi a yau.

“Wannan ita ce babbar damuwata a gare shi. Idan ba yi nasara ba, zan iya ba shi shawara amma zai zama kamar gina wani abu ne bai mai billewa ba.

“Idan na gan shi, zan yi masa fatan alheri ko kuma idan kun gan shi, ku ce masa ina yi masa fatan alheri – amma ya bi a sannu,” in ji Kwankwaso.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a ranar Lahadin da ta gabata ne Tinubu ya bayyana zabar tsohon gwamnan jihar Borno kuma Sanata mai wakiltar Borno ta tsakiya, Kashim Shetima a matsayin abokin takararsa, lamarin da ya haifar da cece-kuce a kan cancanta ko kuma rashin cancantar takarar mutum biyu data addini daya idan aka yi la’akari da kasancewar Nijeriya na da mabambamtan addinai.

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.