ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu

by Sadiq
4 years ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya shawarci dan takarar shugaban kasa a APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da ya kula da lafiyarsa gabanin shiga zaben 2023.

Kwankwaso, wanda tsohon ministan tsaro ne kuma wanda ya mulki jihar Kano sau biyu, yayin wata hira da gidan talabijin na Arise News a ranar Lahadi, ya ce kamata ya yi Tinubu ya kula da lafiyarsa, inda ya yi gargadin cewa yakin neman zaben 2023 zai kasance da tsauri.

  • Goron Sallah: Shugaban APC Ya Yi Wa Nijeriya Addu’ar Zaman Lafiya
  • 2023: Kalubalen Tsaro Na Zama Barazana A Wasu Jihohin Arewacin Nijeriya

“Idan ka ga abokina Bola, ka ce masa ya bi a sannu, ya kula da lafiyarsa sosai… saboda ina sonsa sosai, abokina ne.

ADVERTISEMENT

“Wannan yakin neman zaben zai yi tsauri sosai, yana bukatar jajircewa sosai da dai sauransu. Ina fatan zai yi sauki domin mu ci gaba da fafutukar tabbatar da kasa daya mai karfi da wadata a Nijeriya,” in ji Kwankwaso.

Da aka tambaye shi ko Tinubu na masa barazana, Kwankwaso, wanda shi ne mataimakin kakakin majalisar wakilai a jamhuriya ta uku, ya ce Tinubu a matsayinsa a kashin kansa mutumin kirki ne amma bai san abin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC zai yi daban da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

“Damuwata kawai ita ce jam’iyyar da ya fito. Na san shi mai dabara ne, Bola Tinubu, mutumin kirki ne. Na zauna tare da shi sau da yawa ba za a iya kirgawa ba daga 1992 zuwa yau.

“Ina fatan idan gan shi zan tambaye shi me zai gaya wa ‘yan Nijeriya abin da zai yi na daban da abin da Muhammadu Buhari ke yi a yau.

“Wannan ita ce babbar damuwata a gare shi. Idan ba yi nasara ba, zan iya ba shi shawara amma zai zama kamar gina wani abu ne bai mai billewa ba.

“Idan na gan shi, zan yi masa fatan alheri ko kuma idan kun gan shi, ku ce masa ina yi masa fatan alheri – amma ya bi a sannu,” in ji Kwankwaso.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a ranar Lahadin da ta gabata ne Tinubu ya bayyana zabar tsohon gwamnan jihar Borno kuma Sanata mai wakiltar Borno ta tsakiya, Kashim Shetima a matsayin abokin takararsa, lamarin da ya haifar da cece-kuce a kan cancanta ko kuma rashin cancantar takarar mutum biyu data addini daya idan aka yi la’akari da kasancewar Nijeriya na da mabambamtan addinai.

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Kwankwaso
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.