• Leadership Hausa
Sunday, August 14, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Siyasa

2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu

by Sadiq Usman
1 month ago
in Siyasa
0
2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya shawarci dan takarar shugaban kasa a APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da ya kula da lafiyarsa gabanin shiga zaben 2023.

Kwankwaso, wanda tsohon ministan tsaro ne kuma wanda ya mulki jihar Kano sau biyu, yayin wata hira da gidan talabijin na Arise News a ranar Lahadi, ya ce kamata ya yi Tinubu ya kula da lafiyarsa, inda ya yi gargadin cewa yakin neman zaben 2023 zai kasance da tsauri.

  • Goron Sallah: Shugaban APC Ya Yi Wa Nijeriya Addu’ar Zaman Lafiya
  • 2023: Kalubalen Tsaro Na Zama Barazana A Wasu Jihohin Arewacin Nijeriya

“Idan ka ga abokina Bola, ka ce masa ya bi a sannu, ya kula da lafiyarsa sosai… saboda ina sonsa sosai, abokina ne.

“Wannan yakin neman zaben zai yi tsauri sosai, yana bukatar jajircewa sosai da dai sauransu. Ina fatan zai yi sauki domin mu ci gaba da fafutukar tabbatar da kasa daya mai karfi da wadata a Nijeriya,” in ji Kwankwaso.

Da aka tambaye shi ko Tinubu na masa barazana, Kwankwaso, wanda shi ne mataimakin kakakin majalisar wakilai a jamhuriya ta uku, ya ce Tinubu a matsayinsa a kashin kansa mutumin kirki ne amma bai san abin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC zai yi daban da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.

Labarai Masu Nasaba

Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

“Damuwata kawai ita ce jam’iyyar da ya fito. Na san shi mai dabara ne, Bola Tinubu, mutumin kirki ne. Na zauna tare da shi sau da yawa ba za a iya kirgawa ba daga 1992 zuwa yau.

“Ina fatan idan gan shi zan tambaye shi me zai gaya wa ‘yan Nijeriya abin da zai yi na daban da abin da Muhammadu Buhari ke yi a yau.

“Wannan ita ce babbar damuwata a gare shi. Idan ba yi nasara ba, zan iya ba shi shawara amma zai zama kamar gina wani abu ne bai mai billewa ba.

“Idan na gan shi, zan yi masa fatan alheri ko kuma idan kun gan shi, ku ce masa ina yi masa fatan alheri – amma ya bi a sannu,” in ji Kwankwaso.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a ranar Lahadin da ta gabata ne Tinubu ya bayyana zabar tsohon gwamnan jihar Borno kuma Sanata mai wakiltar Borno ta tsakiya, Kashim Shetima a matsayin abokin takararsa, lamarin da ya haifar da cece-kuce a kan cancanta ko kuma rashin cancantar takarar mutum biyu data addini daya idan aka yi la’akari da kasancewar Nijeriya na da mabambamtan addinai.

Tags: 2023APCKwankwasoNNPPShettimaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Sallah: Shugaban APC Ya Yi Wa Nijeriya Addu’ar Zaman Lafiya

Next Post

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

Related

Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba
Siyasa

Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

15 hours ago
Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe
Siyasa

Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

18 hours ago
Bangar Siyasa Ce Silar Rashin Ci Gaban Arewa –Alhaji Ibrahim
Labarai

Bangar Siyasa Ce Silar Rashin Ci Gaban Arewa –Alhaji Ibrahim

19 hours ago
Rashin Shugabaci Nagari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki, In Ji SDP
Siyasa

Rashin Shugabaci Nagari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki, In Ji SDP

2 days ago
Gwamna Wike Ya Karyata Batun Maka Atiku Da Tambuwal A Kotu
Siyasa

Gwamna Wike Ya Karyata Batun Maka Atiku Da Tambuwal A Kotu

2 days ago
Gwamna Wike Ya Karyata Cire Tutocin PDP Daga Gidan Gwamnatin Jihar Ribas
Siyasa

Gwamna Wike Ya Karyata Cire Tutocin PDP Daga Gidan Gwamnatin Jihar Ribas

2 days ago
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Al’umma Su Ci Gaba Da Gudanar Da Addu’o’in Neman Zaman Lafiya

An Bukaci Al’umma Su Ci Gaba Da Gudanar Da Addu’o’in Neman Zaman Lafiya

August 13, 2022
EFCC Ta Cafke Malaman Addini 2 Da Wasu 5 Kan Zargin Damfara A Yanar Gizo A Kwara

EFCC Ta Cafke Malaman Addini 2 Da Wasu 5 Kan Zargin Damfara A Yanar Gizo A Kwara

August 13, 2022
Fiye Da Miliyan 326 Muka Biya Ma’aikata Da Suka Yi Ritaya A Shekarar Bara -Hukumar Fansho

Fiye Da Miliyan 326 Muka Biya Ma’aikata Da Suka Yi Ritaya A Shekarar Bara -Hukumar Fansho

August 13, 2022
Ganduje Ya Nada Shugabannin Gudanarwa Da Mambobin Hukumar Shari’a

Ganduje Ya Nada Shugabannin Gudanarwa Da Mambobin Hukumar Shari’a

August 13, 2022
Akwai Babban Aiki A Gaban Erik ten Hag A Man U

Akwai Babban Aiki A Gaban Erik ten Hag A Man U

August 13, 2022
Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

August 13, 2022
Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

August 13, 2022
Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

August 13, 2022
Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

August 13, 2022
Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye Ne, Saurayi Ko Budurwa?

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye Ne, Saurayi Ko Budurwa?

August 13, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.