• Leadership Hausa
Saturday, February 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Siyasa

Zabar Mataimaki: Tinubu Ya Watsa Wa Gwamnonin Arewa Maso Yamma Kasa A Ido

by Sadiq
7 months ago
in Siyasa
0
Zabar Mataimaki: Tinubu Ya Watsa Wa Gwamnonin Arewa Maso Yamma Kasa A Ido

A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya zabi tsohon gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima a matsayin wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2023.

Sai dai zabin nasa ya yi fami na gyambon ciwo ga wasu gwamnoni da mabiya a arewa maso yamma.

  • 2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu
  • Ku Kara Kaimi Wajen Inganta Tsaro – Buhari Ga Shugabanni Tsaro

Tun farko a jam’iyyar APC an shiga tsilla-tsilla kan wane ne ya fi dacewa ya yi wa Tinubu takarar mataimaki, lamarin da ya kai ga dan takarar daukar Kabiru Ibrahim Masari a matsayin mataimaki na wucin gadi.

Sai dai shi ma, Masarin ya yi murabus daga mukamin nasa gabanin bayyana daukar Shettima da Tinubu ya yi.

Sai dai wannan hukunci na Tinubu bai yi wa da dama dadi ba, ganin cewar suna da yakinin gwamnonin arewa maso yamma na muhimman mutanen da zasu iya cike masa wancan gibi.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Bayar Da Umarnin A Kamo Mata Shugaban Jam’iyyar APC Na Kano Abdullahi Abbas

Ka Mutunta Girmanka, Ka Janyewa Kwankwaso — Martanin NNPP Ga Atiku

Wasu magoya baya na ganin cewar gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje na iya zama mataimakin Tinubu a zaben 2023, duba da irin gudunmawar da ya ba shi.

Wasu na ganin Ganduje yayi bajinta sosai tun farkon fara tafiyar Tinubu ta nuna son yi takarar shugaban kasa, inda suke da yakinin cewar gwamnan na Kano, na da gogewa da kuma duk abin da ake bukata sama da zabin na Tinubu (Shettima).

Wasu kuma na ganin cewar gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, shi ne zabin da zai sa APC ta jijjiga jam’iyyar adawa ta PDP a babban zaben 2023.

Da fari wasu sun fara kiraye-kirayen da Tinubu ya dauki gwamnan na Kaduna, sai dai ba a san me ya faru aka haihu a ragaya ba.

A tunani irin na wadancan masu son Tinubu ya dauki El-Rufai, sun bayyana cewar gwamnan ya zama zakaran gwajin-dafi idan aka kwatanta shi da duk gwamnonin Nijeriya, wajen sanin salon shugabanci da kuma kware wajen sarrafa ayyukan ci gaba, musamman idan aka yi duba da yadda ya sauya fasalin birnin tarayya Abuja, lokacin da ya rike mukamin minista.

A wani kaulin kuwa, wasu masu sharhin siyasa na ganin Badaru Abubakar na jihar Jigawa, na iya zama mataimakin takarar Tinubu.

Wannan tunani nasu ba zai rasa nasaba da irin gudunmawar da a gwamnan na Jigawa ya bayar wajen farfado da jam’iyyar daga gargarar mutuwa a lokacin da ta ke fama da rikice-rikicen cikin gida ba.

Gwamnan na daga cikin mambobin kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar karkashin jagorancin Mai Mala Buni.

Har ila yau, suna ganin janyewa Tinubu takarar shugaban kasa da gwamnan yayi a zaben fidda-gwanin APC, wannan ma wata alama ce da ke nuni da dacewar a zabe shi.

Sai dai duk da wannan kiraye-kiraye da wasu ke yi na zabar daya daga cikin gwamnonin na arewa maso yamma bai yi tasiri ba, domin kuwa Tinubu ya kunnen uwar shegu da su.

Tsohon gwamnan na Legas, ya zabi shugaban yakin neman zabensa na takarar shugaban kasa.

Tags: 2023BadaruEl-RufaiGandujeJigawaKadunakanoKashim ShettimaMataimakiTakarar Shugaban KasaTinubuZabe
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 18 A Zamfara, Mutane Sun Tsere Daga Gidajensu

Next Post

Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

Related

Kotu Ta Bayar Da Umarnin A Kamo Mata Shugaban Jam’iyyar APC Na Kano Abdullahi Abbas
Siyasa

Kotu Ta Bayar Da Umarnin A Kamo Mata Shugaban Jam’iyyar APC Na Kano Abdullahi Abbas

1 day ago
Ka Mutunta Girmanka, Ka Janyewa Kwankwaso — Martanin NNPP Ga Atiku
Siyasa

Ka Mutunta Girmanka, Ka Janyewa Kwankwaso — Martanin NNPP Ga Atiku

2 days ago
Aisha Buhari Ta Goyi Bayan El-rufai Kan Zargin Yi Wa Tunibu Zagon Kasa A Fadar Shugaban Kasa
Siyasa

Aisha Buhari Ta Goyi Bayan El-rufai Kan Zargin Yi Wa Tunibu Zagon Kasa A Fadar Shugaban Kasa

2 days ago
PDP Za Ta Fatattaki Jam’iyyar APC Daga Gidan Gwamnatin Jihar Kaduna –Makarfi
Siyasa

PDP Za Ta Fatattaki Jam’iyyar APC Daga Gidan Gwamnatin Jihar Kaduna –Makarfi

2 days ago
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar
Siyasa

‘Yan Majalisar Tarayya 3 Na Jam’iyyar APC Sun Koma Jam’iyyar PDP A Jihar Katsina

4 days ago
Tinubu Ya Godewa Buhari Kan Amincewa Da Kara Wa’adin Kwanakin Daina Karbar Tsoffin Kudade
Siyasa

Tinubu Ya Godewa Buhari Kan Amincewa Da Kara Wa’adin Kwanakin Daina Karbar Tsoffin Kudade

5 days ago
Next Post
Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

LABARAI MASU NASABA

ICPC Ta Cafke Ma’aikatan Banki Da Wasu Kan Boye Sabbin Kudi A Abuja Da Osun 

ICPC Ta Cafke Ma’aikatan Banki Da Wasu Kan Boye Sabbin Kudi A Abuja Da Osun 

February 3, 2023
‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sa-kai 41 A Katsina

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sa-kai 41 A Katsina

February 3, 2023
Sin Ta Bukaci Japan Ta Cika Alkawarin Ta Tare Da Yin Abun Da Ya Dace Kan Muhimman Batutuwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Cika Alkawarin Ta Tare Da Yin Abun Da Ya Dace Kan Muhimman Batutuwa

February 3, 2023
Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike

Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike

February 3, 2023
Ya Kamata Amurka Ta Nuna Girmamawa Yayin Sake Bude Ofishin Jakadancinta A Solomon

Ya Kamata Amurka Ta Nuna Girmamawa Yayin Sake Bude Ofishin Jakadancinta A Solomon

February 3, 2023
Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari

Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari

February 3, 2023
Ana Gab Da Gabatar Da Kumfyutar Quantum Na Sin Mai Suna Wukong

Ana Gab Da Gabatar Da Kumfyutar Quantum Na Sin Mai Suna Wukong

February 3, 2023
CMG Zai Nuna Bikin Kunna Fitilu Na Shekarar 2023 Da Yammacin Ranar Lahadi

CMG Zai Nuna Bikin Kunna Fitilu Na Shekarar 2023 Da Yammacin Ranar Lahadi

February 3, 2023
Sin Za Ta Fadada Shigo Da Hajoji Masu Nagarta A Shekarar Nan Ta 2023

Sin Za Ta Fadada Shigo Da Hajoji Masu Nagarta A Shekarar Nan Ta 2023

February 3, 2023
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

February 3, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.