ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabar Mataimaki: Tinubu Ya Watsa Wa Gwamnonin Arewa Maso Yamma Kasa A Ido

by Sadiq
4 years ago
Tinubu

A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya zabi tsohon gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima a matsayin wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2023.

Sai dai zabin nasa ya yi fami na gyambon ciwo ga wasu gwamnoni da mabiya a arewa maso yamma.

  • 2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu
  • Ku Kara Kaimi Wajen Inganta Tsaro – Buhari Ga Shugabanni Tsaro

Tun farko a jam’iyyar APC an shiga tsilla-tsilla kan wane ne ya fi dacewa ya yi wa Tinubu takarar mataimaki, lamarin da ya kai ga dan takarar daukar Kabiru Ibrahim Masari a matsayin mataimaki na wucin gadi.

ADVERTISEMENT

Sai dai shi ma, Masarin ya yi murabus daga mukamin nasa gabanin bayyana daukar Shettima da Tinubu ya yi.

Sai dai wannan hukunci na Tinubu bai yi wa da dama dadi ba, ganin cewar suna da yakinin gwamnonin arewa maso yamma na muhimman mutanen da zasu iya cike masa wancan gibi.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Wasu magoya baya na ganin cewar gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje na iya zama mataimakin Tinubu a zaben 2023, duba da irin gudunmawar da ya ba shi.

Wasu na ganin Ganduje yayi bajinta sosai tun farkon fara tafiyar Tinubu ta nuna son yi takarar shugaban kasa, inda suke da yakinin cewar gwamnan na Kano, na da gogewa da kuma duk abin da ake bukata sama da zabin na Tinubu (Shettima).

Wasu kuma na ganin cewar gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, shi ne zabin da zai sa APC ta jijjiga jam’iyyar adawa ta PDP a babban zaben 2023.

Da fari wasu sun fara kiraye-kirayen da Tinubu ya dauki gwamnan na Kaduna, sai dai ba a san me ya faru aka haihu a ragaya ba.

A tunani irin na wadancan masu son Tinubu ya dauki El-Rufai, sun bayyana cewar gwamnan ya zama zakaran gwajin-dafi idan aka kwatanta shi da duk gwamnonin Nijeriya, wajen sanin salon shugabanci da kuma kware wajen sarrafa ayyukan ci gaba, musamman idan aka yi duba da yadda ya sauya fasalin birnin tarayya Abuja, lokacin da ya rike mukamin minista.

A wani kaulin kuwa, wasu masu sharhin siyasa na ganin Badaru Abubakar na jihar Jigawa, na iya zama mataimakin takarar Tinubu.

Wannan tunani nasu ba zai rasa nasaba da irin gudunmawar da a gwamnan na Jigawa ya bayar wajen farfado da jam’iyyar daga gargarar mutuwa a lokacin da ta ke fama da rikice-rikicen cikin gida ba.

Gwamnan na daga cikin mambobin kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar karkashin jagorancin Mai Mala Buni.

Har ila yau, suna ganin janyewa Tinubu takarar shugaban kasa da gwamnan yayi a zaben fidda-gwanin APC, wannan ma wata alama ce da ke nuni da dacewar a zabe shi.

Sai dai duk da wannan kiraye-kiraye da wasu ke yi na zabar daya daga cikin gwamnonin na arewa maso yamma bai yi tasiri ba, domin kuwa Tinubu ya kunnen uwar shegu da su.

Tsohon gwamnan na Legas, ya zabi shugaban yakin neman zabensa na takarar shugaban kasa.

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.