ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabar Mataimaki: Tinubu Ya Watsa Wa Gwamnonin Arewa Maso Yamma Kasa A Ido

by Sadiq
4 years ago
Tinubu

A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya zabi tsohon gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima a matsayin wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2023.

Sai dai zabin nasa ya yi fami na gyambon ciwo ga wasu gwamnoni da mabiya a arewa maso yamma.

  • 2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu
  • Ku Kara Kaimi Wajen Inganta Tsaro – Buhari Ga Shugabanni Tsaro

Tun farko a jam’iyyar APC an shiga tsilla-tsilla kan wane ne ya fi dacewa ya yi wa Tinubu takarar mataimaki, lamarin da ya kai ga dan takarar daukar Kabiru Ibrahim Masari a matsayin mataimaki na wucin gadi.

ADVERTISEMENT

Sai dai shi ma, Masarin ya yi murabus daga mukamin nasa gabanin bayyana daukar Shettima da Tinubu ya yi.

Sai dai wannan hukunci na Tinubu bai yi wa da dama dadi ba, ganin cewar suna da yakinin gwamnonin arewa maso yamma na muhimman mutanen da zasu iya cike masa wancan gibi.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Wasu magoya baya na ganin cewar gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje na iya zama mataimakin Tinubu a zaben 2023, duba da irin gudunmawar da ya ba shi.

Wasu na ganin Ganduje yayi bajinta sosai tun farkon fara tafiyar Tinubu ta nuna son yi takarar shugaban kasa, inda suke da yakinin cewar gwamnan na Kano, na da gogewa da kuma duk abin da ake bukata sama da zabin na Tinubu (Shettima).

Wasu kuma na ganin cewar gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, shi ne zabin da zai sa APC ta jijjiga jam’iyyar adawa ta PDP a babban zaben 2023.

Da fari wasu sun fara kiraye-kirayen da Tinubu ya dauki gwamnan na Kaduna, sai dai ba a san me ya faru aka haihu a ragaya ba.

A tunani irin na wadancan masu son Tinubu ya dauki El-Rufai, sun bayyana cewar gwamnan ya zama zakaran gwajin-dafi idan aka kwatanta shi da duk gwamnonin Nijeriya, wajen sanin salon shugabanci da kuma kware wajen sarrafa ayyukan ci gaba, musamman idan aka yi duba da yadda ya sauya fasalin birnin tarayya Abuja, lokacin da ya rike mukamin minista.

A wani kaulin kuwa, wasu masu sharhin siyasa na ganin Badaru Abubakar na jihar Jigawa, na iya zama mataimakin takarar Tinubu.

Wannan tunani nasu ba zai rasa nasaba da irin gudunmawar da a gwamnan na Jigawa ya bayar wajen farfado da jam’iyyar daga gargarar mutuwa a lokacin da ta ke fama da rikice-rikicen cikin gida ba.

Gwamnan na daga cikin mambobin kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar karkashin jagorancin Mai Mala Buni.

Har ila yau, suna ganin janyewa Tinubu takarar shugaban kasa da gwamnan yayi a zaben fidda-gwanin APC, wannan ma wata alama ce da ke nuni da dacewar a zabe shi.

Sai dai duk da wannan kiraye-kiraye da wasu ke yi na zabar daya daga cikin gwamnonin na arewa maso yamma bai yi tasiri ba, domin kuwa Tinubu ya kunnen uwar shegu da su.

Tsohon gwamnan na Legas, ya zabi shugaban yakin neman zabensa na takarar shugaban kasa.

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

Bukukuwan Babbar Sallah: Wane Tanadi Matasa Suka Yi?

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.