• English
  • Business News
Thursday, May 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Atiku Da Obi Sun Shigar Da Kara Ta Kalubalantar Nasarar Tinubu

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Zaben 2023: Atiku Da Obi Sun Shigar Da Kara Ta Kalubalantar Nasarar Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jagororin manyan jami’iyyun adawa biyu; PDP da LP, sun shigar da kara a kan neman soke sakamakon zaben shugaban kasa na watan Fabrairu da suke kalubalanta, kamar yadda takardun kotu suka nuna, domin fara wata shari’ar da ka iya daukar tsawon watanni.

An shigar da kararraki da dama na kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar Nijeriya, amma ga dukkan alamu babu wadda ta yi nasara.

  • NIS Reshen Ribas Ta Kafa Kwamitin Bunkasa Walwalar Jami’ai
  • Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

Dan takarar babbar jami’iyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar da Peter Obi na jami’iyar Labour Party, sun roki kotun daukaka kara da ta soke zaben da Bola Tinubu dan takarar jami’iyar APC ya lashe.

Shugabannin jami’iyyun adawan sun fada a wata takardar rantsuwar kotu cewa zaben na tattare da magudi kana sun zargi hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC da take doka, inda ta gaza amfani da na’urar lantarki wajen daukar sakamakon zabe daga runfunan zabe da ma wasu zargi zargin.

Atiku da Obi sun nemi umarnin kotu kan sako bayanan zaben shugaban kasa, kana INEC ta gudanar da sabon zabe.

Labarai Masu Nasaba

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Tinubu ya kare zaben da cewa an gudanar da shi cikin adalci.

Obi da ya shigo takara a karon farko, ya samu goyon bayan matasa da sababbin masu kada kuri’a kuma da alamar ya fadada takarar, inda ya bai wa masu zabe kwarin gwiwar samun sauyi daga shekaru na wahala da tashin hankali karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari mai shekaru 80, tsohon Janar na soja.

Amma Obi ya zo na uku bayan Tinubu da Atiku, wanda dukkaninsu nada jami’iyyu siyasa masu karfi da kuma gomman shekaru na harkokin siyasa.

APC da PDP sune suka gudanar da mulkin Najeriya tsakaninsu tun bayan karshen mulkin soja a shekarar 1999.

Masu sa ido a kan zaben sun zargi INEC da rashin cikakken shiri da kuma jinkiri wurin fara zabe amma basu yi zargin tafka magudi ba. Hukumar kanta ta roki gafara a kan matsalolin na’ura da ta fuskanta wurin kidaya.

Kotun daukaka karar tana da kwanaki 180 ta saurari karar kana ta zartar da hukunci a karar da Obi ya shigar ta kalubalantar sakamakon.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuKotuPeter ObitinuubuZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Reshen Ribas Ta Kafa Kwamitin Bunkasa Walwalar Jami’ai

Next Post

Emefiele Ya Roki Gafarar ‘Yan Nijeriya Kan Matsalar Hada-Hadar Kudi Ta Intanet

Related

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

4 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

4 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

7 hours ago
APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo
Manyan Labarai

APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo

1 day ago
Kwanaki 40: Iyalan Maharban Da Aka Kashe A Edo Na Neman A Biya Su Diyya
Manyan Labarai

Kwanaki 40: Iyalan Maharban Da Aka Kashe A Edo Na Neman A Biya Su Diyya

1 day ago
Za Mu Magance Matsalar Ruwan Sha Kafin Ƙarshen 2025 A Kaduna – Uba Sani
Manyan Labarai

Za Mu Magance Matsalar Ruwan Sha Kafin Ƙarshen 2025 A Kaduna – Uba Sani

1 day ago
Next Post
Emefiele Ya Roki Gafarar ‘Yan Nijeriya Kan Matsalar Hada-Hadar Kudi Ta Intanet

Emefiele Ya Roki Gafarar 'Yan Nijeriya Kan Matsalar Hada-Hadar Kudi Ta Intanet

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

May 8, 2025
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

May 8, 2025
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.