• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Sojoji, ‘Yansanda Za Su Samar Da Ingantaccen Tsaro – GOC 

by Sadiq
3 years ago
Zaben 2023

Rundunar sojin Nijeriya ta jaddada kudirinta na hada kai da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro domin ganin an gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali. 

Babban kwamandan rundunar sojojin Nijeriya ta 7, Manjo-Janar Waidi Shuaib ne, ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga kwamishinan ‘yansandan Jihar Borno, Abdu Umar a ranar Talata a Maiduguri.

  • Ta’addanci Ya Zama Tarihi, Nijeriya Na Cikin Aminci – Lai Muhammad
  • Ambaliyar Ruwa: Jihohi 21 Sun Samu Kayayyakin Agaji –Sadiya Farouq

Ya ce hada gwiwa tsakanin sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro zai taimaka wajen samar da ingantaccen tsaro kafin zabe da kuma bayan zabe a kasar.

GOC ya ce ziyarar za ta ba shi damar kara kaimin tunani game da shirye-shiryen ‘yansanda don magance matsalolin tsaro a lokacin zabe.

“Hukumar ‘yansanda ita ce kan gaba amma saboda yanayin yankin Arewa-maso-Gabas ke ciki, ya bukaci sojoji da su jagoranci ayyuka daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

“Rikicin zabe na iya faruwa ko dai kafin gudanar da zabukan, ko a lokacin a lokacin zabe ko bayan zabe, kuma dukkanin hukumomin biyu za su hada hannu wajen magance wadannan matsalolin.

“Kamar yadda aka fara yakin neman zabe, jami’an tsaro na hadin gwiwa sukan gudanar da ayyuka don tabbatar da cewa babban birnin ya kasance lafiya.

“Za mu so mu tabbatar da kuma karfafa dukkan sojojinmu ciki har da rundunonin sojan hadin gwiwa domin samun ingantaccen muhalli a cikin birnin Maiduguri.

“An samj rahoton sirri da yawa. Sai dai idan muka yi aiki tare za a tabbatar da cewa abubuwa sun tafi yadda suka dace,” in ji shi.

Da yake mayar da martani, Abdu ya ce ‘yansandan za su ci gaba da hada kai da sojoji domin kare rayuka da dukiyoyi a jihar.

Ya ce rundunar ta karfafa sintiri tare da hadin gwiwar rundunonin sojoji domin yaki da miyagun laifuka a cikin babban birnin Maiduguri.

Kwamishinan ya sake nanata shirye-shiryen ‘yansanda na samar da tsaro domin saukaka gudanar da zabe cikin gaskiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Next Post
An Ceto Wasu ‘Yansanda 3 Da Aka Sace A Kuros Riba 

An Ceto Wasu 'Yansanda 3 Da Aka Sace A Kuros Riba 

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.