• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Sojoji, ‘Yansanda Za Su Samar Da Ingantaccen Tsaro – GOC 

by Sadiq
3 years ago
Zaben 2023

Rundunar sojin Nijeriya ta jaddada kudirinta na hada kai da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro domin ganin an gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali. 

Babban kwamandan rundunar sojojin Nijeriya ta 7, Manjo-Janar Waidi Shuaib ne, ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga kwamishinan ‘yansandan Jihar Borno, Abdu Umar a ranar Talata a Maiduguri.

  • Ta’addanci Ya Zama Tarihi, Nijeriya Na Cikin Aminci – Lai Muhammad
  • Ambaliyar Ruwa: Jihohi 21 Sun Samu Kayayyakin Agaji –Sadiya Farouq

Ya ce hada gwiwa tsakanin sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro zai taimaka wajen samar da ingantaccen tsaro kafin zabe da kuma bayan zabe a kasar.

GOC ya ce ziyarar za ta ba shi damar kara kaimin tunani game da shirye-shiryen ‘yansanda don magance matsalolin tsaro a lokacin zabe.

“Hukumar ‘yansanda ita ce kan gaba amma saboda yanayin yankin Arewa-maso-Gabas ke ciki, ya bukaci sojoji da su jagoranci ayyuka daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

“Rikicin zabe na iya faruwa ko dai kafin gudanar da zabukan, ko a lokacin a lokacin zabe ko bayan zabe, kuma dukkanin hukumomin biyu za su hada hannu wajen magance wadannan matsalolin.

“Kamar yadda aka fara yakin neman zabe, jami’an tsaro na hadin gwiwa sukan gudanar da ayyuka don tabbatar da cewa babban birnin ya kasance lafiya.

“Za mu so mu tabbatar da kuma karfafa dukkan sojojinmu ciki har da rundunonin sojan hadin gwiwa domin samun ingantaccen muhalli a cikin birnin Maiduguri.

“An samj rahoton sirri da yawa. Sai dai idan muka yi aiki tare za a tabbatar da cewa abubuwa sun tafi yadda suka dace,” in ji shi.

Da yake mayar da martani, Abdu ya ce ‘yansandan za su ci gaba da hada kai da sojoji domin kare rayuka da dukiyoyi a jihar.

Ya ce rundunar ta karfafa sintiri tare da hadin gwiwar rundunonin sojoji domin yaki da miyagun laifuka a cikin babban birnin Maiduguri.

Kwamishinan ya sake nanata shirye-shiryen ‘yansanda na samar da tsaro domin saukaka gudanar da zabe cikin gaskiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya
Manyan Labarai

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

October 24, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Next Post
An Ceto Wasu ‘Yansanda 3 Da Aka Sace A Kuros Riba 

An Ceto Wasu 'Yansanda 3 Da Aka Sace A Kuros Riba 

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

October 24, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.