ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Jihohi 21 Sun Samu Kayayyakin Agaji –Sadiya Farouq

by Sulaiman
4 years ago
Sadiya Farouq

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana cewa ma’aikatar ta rarraba kayan agaji ga dukkan jihohi 21 da bala’in ambaliyar ruwa ta shafa a sassa daban-daban na ƙasar nan a bana.

Ministar ta bayyana hakan ne a wajen taron da ta yi da manema labarai a ranar Talata a ofishin ta a Abuja domin bayyana irin ayyukan jinƙai da ma’aikatar, tare da haɗin gwiwa da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa (NEMA), su ka kai a wuraren da ambaliyar ta shafa.

  • Karramawar Shugaban Kasa Ta Kara Min Ƙaimi – Sadiya Farouq

Ministar ta ce, “Zuwa yanzu jihohi 21 sun karɓi nasu kayan agajin, waɗanda su ka haɗa da Abiya, Adamawa, Anambara, Bayalsa, Ekiti, Inugu, Imo, Jigawa,
Kaduna, Kano, Kwara, Legas, Nasarawa, Neja, Ogun, Ondo, Oyo, Sakkwato, Taraba, Yobe da Gundumar Birnin Tarayya.”

ADVERTISEMENT

Hajiya Sadiya ta ce sakamakon bala’in ambaliyar, kimanin mutum 1,427,370 su ka rasa matsugunan su, wasu 612 kuma su ka rasa rayukan su, sannan wasu 2,776 su ka samu raunuka.

Sadiya Farouq

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ta ƙara da cewa yanzu haka akwai ƙwararru da ke gudanar da irin waɗannan ayyuka, musamman ganin cewa har yanzu akwai wasu Ƙananan Hukumomi da ba sa shiguwa saboda matsalar ambaliyar.

Ta ce: “Domin samun nasarar wannan aiki, mun haɗa hannu da sashen kai agaji na sojojin ƙasar nan, tare da sauran ƙwararru da ingantattun kayan aiki, domin amfani da su wajen isa ga wurare masu wuyar zuwa da kuma jama’ar da ke cikin haɗari.”

Ministar ta ba da tabbacin cewa har yanzu ana ci gaba da wannan aiki na kai kayan agaji ga jihohin da wannan ambaliya ta shafa.

Yayin da ta ke ƙarin haske game da kayan da ma’aikatar ta raba, ministar ta ce, “Abubuwan da mu ka raba, kaya ne na buƙatar gaggawa na abinci, waɗanda su ka haɗa da shinkafa, masara, garin rogo, man gyaɗa, wake da kayan dafa abinci.

“Kayan da ba na abinci ba kuma da aka kai domin samun matsuguni na wucin-gadi ga jama’ar da su ka rasa wurin zama sun haɗa da kwanon rufi, siminti, kusoshi, sili, barguna, tabarmin roba da kwano.”

Haka kuma ministar ta ce ma’aikatan ceto su na nan su na aiki wurjanjan tun da aka fara ambaliyar, su na kwashe wadanda bala’in ya shafa tare da sama masu matsuguni, kuma ana kai wasu asibiti domin su samu kula ba tare da bata lokaci ba.

Sadiya Farouq

Ta yi kira ga sauran masu ruwa da tsaki a lamarin da su shigo cikin ƙoƙarin da ake yi na taimaka wa wadanda abin ya shafa. Ta ce, “Fatan mu shi ne sauran ma’aikatun gwamnati irin su Ma’aikatar Albarkatun Kiwon Lafiya, Ayyuka da Gidaje, Aikin Gona, da Yanayi za su zo mu hada gwiwa a taron manema labarai na gaba domin su ma su gabatar da nasu bayanan kan ayyuka su domin mu yi bayani kan wannan aikin agaji da mu ke yi.

“Ina yin kira kuma ga gwamnatoci a kowane mataki, musamman na jihohi da ƙananan hukumomi, da su ba ‘yan sanda da mu bayanan da su ka dace, sannan su taka rawa wajen aikin ceto, kamar yadda Tsarin Gaggawa kan Shirya wa Ambaliya da Ceto na Kasa ya tanadar, wato ‘Flood Emergency Preparedness and Response Plan’.

“Ina jinjina wa jama’ar garuruwa saboda dagewar su. Mun samu rahoton cewa a cikin ƙananan hukumomi 144, jama’a a garuruwa sun yi aiki tare wajen samar da agajin farko ga iyalan su da maƙwatan su.

“Tawagar masu aikin bincikowa da ceto jama’a, waɗanda aikin ɗauko jama’a da ba su agajin farko don ceton rayuwar su tare da ba su magani da takardar zuwa asibiti ya rataya a wuyan su, ya zuwa yanzu sun isa yankunan ƙananan hukumomi 199 a jihohi 25.

“Ana ci gaba da aiwatar da waɗannan ayyuka kuma ina kira ga jama’ar garuruwan da ke cikin haɗarin aukuwar bala’i da su tabbatar da sun bi gargaɗi da umarnin da waɗannan ma’aikatan su ke ba su domin su na aiki ne saboda su kare tare da ceto rayuka.

Sadiya Farouq

Ministar ta mika Godiya ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari saboda “goyon bayan da ya ba mu tare da ɗaukar mataki da sauri wajen magance matsalolin ambaliya.”

Ta ƙara da cewa: “Wata babbar tawaga za ta ziyarci wasu daga jihohin a makon gobe domin ɗorawa kan ayyukan ceto da agaji tare da gano sababbin matsaloli da kurakurai a ayyukan waɗanda ke bukatar a gyara su. Hakan zai ba gwamnati damar nazartar al’amarin a kurkusa tare da haɗuwa da waɗanda abin ya shafa da iyalan su.”

Sadiya Farouq
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Ta’addanci Ya Zama Tarihi, Nijeriya Na Cikin Aminci – Lai Muhammad

Ta'addanci Ya Zama Tarihi, Nijeriya Na Cikin Aminci - Lai Muhammad

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.