ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Sojoji, ‘Yansanda Za Su Samar Da Ingantaccen Tsaro – GOC 

by Sadiq
4 years ago
Zaben 2023

Rundunar sojin Nijeriya ta jaddada kudirinta na hada kai da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro domin ganin an gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali. 

Babban kwamandan rundunar sojojin Nijeriya ta 7, Manjo-Janar Waidi Shuaib ne, ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga kwamishinan ‘yansandan Jihar Borno, Abdu Umar a ranar Talata a Maiduguri.

  • Ta’addanci Ya Zama Tarihi, Nijeriya Na Cikin Aminci – Lai Muhammad
  • Ambaliyar Ruwa: Jihohi 21 Sun Samu Kayayyakin Agaji –Sadiya Farouq

Ya ce hada gwiwa tsakanin sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro zai taimaka wajen samar da ingantaccen tsaro kafin zabe da kuma bayan zabe a kasar.

ADVERTISEMENT

GOC ya ce ziyarar za ta ba shi damar kara kaimin tunani game da shirye-shiryen ‘yansanda don magance matsalolin tsaro a lokacin zabe.

“Hukumar ‘yansanda ita ce kan gaba amma saboda yanayin yankin Arewa-maso-Gabas ke ciki, ya bukaci sojoji da su jagoranci ayyuka daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

“Rikicin zabe na iya faruwa ko dai kafin gudanar da zabukan, ko a lokacin a lokacin zabe ko bayan zabe, kuma dukkanin hukumomin biyu za su hada hannu wajen magance wadannan matsalolin.

“Kamar yadda aka fara yakin neman zabe, jami’an tsaro na hadin gwiwa sukan gudanar da ayyuka don tabbatar da cewa babban birnin ya kasance lafiya.

“Za mu so mu tabbatar da kuma karfafa dukkan sojojinmu ciki har da rundunonin sojan hadin gwiwa domin samun ingantaccen muhalli a cikin birnin Maiduguri.

“An samj rahoton sirri da yawa. Sai dai idan muka yi aiki tare za a tabbatar da cewa abubuwa sun tafi yadda suka dace,” in ji shi.

Da yake mayar da martani, Abdu ya ce ‘yansandan za su ci gaba da hada kai da sojoji domin kare rayuka da dukiyoyi a jihar.

Ya ce rundunar ta karfafa sintiri tare da hadin gwiwar rundunonin sojoji domin yaki da miyagun laifuka a cikin babban birnin Maiduguri.

Kwamishinan ya sake nanata shirye-shiryen ‘yansanda na samar da tsaro domin saukaka gudanar da zabe cikin gaskiya.

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
An Ceto Wasu ‘Yansanda 3 Da Aka Sace A Kuros Riba 

An Ceto Wasu 'Yansanda 3 Da Aka Sace A Kuros Riba 

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.