• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023 Zai Zama Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya, In Ji INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Zaben 2023 Zai Zama Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya, In Ji INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bada tabbacin cewa manyan zaɓuɓɓukan da za a yi a Nijeriya a baɗi sai sun fi duk waɗanda aka yi a baya nagarta.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya faɗi haka a ranar Talata a Abuja lokacin da ya karɓi baƙuncin jami’an wasu hukumomin tsara harkar zaɓe da su ka zo daga Amurka, wato ‘International Republican Institute’ (IRI) da
‘National Democratic Institute’ (NDI).

  • Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Ya ce zaman da su ka yi da maziyartan shi ne na karo na farko da INEC ta karɓi baƙuncin wasu masu ruwa da tsaki a harkar zaɓe tun bayan zaɓen gwamnan Jihar Osun da aka yi a ran Asabar, kuma ya yi alƙawarin hukumar za ta ɗora a kan nasarorin da ta samu a zaɓuɓɓuka masu zuwa.

INEC

Farfesa Yakubu ya faɗa wa maziyartan nasa cewa: “Kyawawan kalaman ku sun ƙara mana ƙwarin gwiwa, amma har yanzu akwai babban aiki a gaban mu.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

“Mu na ba ku tabbacin cewa za mu ci gaba da aiki tuƙuru fiye ma da na da domin gudanar da manyan zaɓuɓɓukan 2023.

“Na saurari wasu daga cikin batutuwan da aka gabatar a nan, amma ƙila idan mun shiga zaman aikin da za mu yi akwai damar da za mu samu mu yi tsokaci kan wasu daga cikin batutuwan.’’

Yakubu ya kuma yi magana kan zaɓuɓɓukan gwamna da aka yi a Ekiti a watan Yuni da na Osun da aka yi a ranar Asabar.

Ya ce: “Dangane da shirin manyan zaɓuɓɓukan 2023, ina so in tabbatar maku da cewa sai da mu ka yi wa ‘yan Nijeriya alƙawarin cewa zaɓen Ekiti zai yi kyau, kuma sai ga shi zaɓen na Ekiti ya yi kyau. Mun yi alƙawarin zaɓen Osun zai ma fi kyau, sai ga shi zaɓen na Osun ya yi kyau fiye da wanda ya gabace shi.

“Yanzu mu na maku alƙawarin cewa manyan zaɓuɓɓukan 2023 za su fi duk wani zaɓe da mu ka yi a baya inganci kuma mun sadaukar da kan mu wajen gudanar da zaɓe mafi nagarta.”

Tun da farko, sai da jagoran maziyartan, Mista Frank LaRose, wanda shi ne Sakataren Jihar Ohio ta ƙasar Amurka, ya yaba wa INEC kan ƙoƙarin da ta ke yi na inganta al’amarin zaɓe a Nijeriya.

LaRose, wanda kuma kwamishinan zaɓe ne a Jihar ta Ohio, ya bayyana wannan ziyara da ya fara kawowa a Nijeriya a matsayin wata babbar dama da ya samu ta koyon abubuwa. Ya yi kira ga INEC da ta ci gaba da inganta tsarin zaɓe na Nijeriya.

INEC

Ya ce: “Ina jagorantar maziyarta waɗanda manyan masana ne a harkar zaɓe daga yankin mu, da ma faɗin Amurka.

“Waɗannan maziyartan su na da tunani irin naku na cewa mutanen Nijeriya sun cancanci su ci gaba da samun zaɓe mai inganci babu murɗiya, karɓaɓɓe ga kowa, saboda haka mu na aiki domin shirya wa zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023.

“Mun samu damar kai ziyara a Osun saboda wannan shi ne karo na biyu da aka gudanar da zaɓe a ƙarƙashin sabuwar Dokar Zaɓe.

“Mun haɗu da Kwamishinan Zaɓe Mazaunin can (REC) a Osun kuma mun yi nazarin wuraren kaɗa ƙuri’a daban-daban a Ranar Zaɓe.

“Da farko dai, ina so in yaba wa dukkan ku saboda aikin da ku ke ci gaba da gudanarwa wanda za ku ci gaba da inganta shi. Mun san cewa a ko yaushe akwai buƙatar a inganta aiki.

“Sai dai kuma, akwai buƙatar mu fara da yin la’akari da ingancin da INEC ta ke ta ƙara samu don gudanar da zaɓe mai kyau; kuma wannan wani abu ne da mu ka gani da idanuwan mu, ba wai mun jira wani ya zo ya ba mu labari ba ne.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Gidajen Burodi Na Shirin Tsunduma Yajin Aiki

Next Post

Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok A Borno

Related

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi
Labarai

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

2 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu
Manyan Labarai

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

4 hours ago
Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe
Labarai

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

6 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

8 hours ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

9 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

11 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok A Borno

Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin 'Yan Matan Chibok A Borno

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

June 17, 2025
An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

June 17, 2025
Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

June 17, 2025
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

June 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

June 17, 2025
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

June 17, 2025
Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

June 17, 2025
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

June 17, 2025
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

June 17, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.