• Leadership Hausa
Sunday, October 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023 Zai Zama Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya, In Ji INEC

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Zaben 2023 Zai Zama Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya, In Ji INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bada tabbacin cewa manyan zaɓuɓɓukan da za a yi a Nijeriya a baɗi sai sun fi duk waɗanda aka yi a baya nagarta.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya faɗi haka a ranar Talata a Abuja lokacin da ya karɓi baƙuncin jami’an wasu hukumomin tsara harkar zaɓe da su ka zo daga Amurka, wato ‘International Republican Institute’ (IRI) da
‘National Democratic Institute’ (NDI).

  • Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Ya ce zaman da su ka yi da maziyartan shi ne na karo na farko da INEC ta karɓi baƙuncin wasu masu ruwa da tsaki a harkar zaɓe tun bayan zaɓen gwamnan Jihar Osun da aka yi a ran Asabar, kuma ya yi alƙawarin hukumar za ta ɗora a kan nasarorin da ta samu a zaɓuɓɓuka masu zuwa.

INEC

Farfesa Yakubu ya faɗa wa maziyartan nasa cewa: “Kyawawan kalaman ku sun ƙara mana ƙwarin gwiwa, amma har yanzu akwai babban aiki a gaban mu.

Labarai Masu Nasaba

Somaliya Da ATMIS Sun Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Tsakiyar Kasar

Kotu Ta Tabbatar Da Kefas A Matsayin Gwamnan Taraba

“Mu na ba ku tabbacin cewa za mu ci gaba da aiki tuƙuru fiye ma da na da domin gudanar da manyan zaɓuɓɓukan 2023.

“Na saurari wasu daga cikin batutuwan da aka gabatar a nan, amma ƙila idan mun shiga zaman aikin da za mu yi akwai damar da za mu samu mu yi tsokaci kan wasu daga cikin batutuwan.’’

Yakubu ya kuma yi magana kan zaɓuɓɓukan gwamna da aka yi a Ekiti a watan Yuni da na Osun da aka yi a ranar Asabar.

Ya ce: “Dangane da shirin manyan zaɓuɓɓukan 2023, ina so in tabbatar maku da cewa sai da mu ka yi wa ‘yan Nijeriya alƙawarin cewa zaɓen Ekiti zai yi kyau, kuma sai ga shi zaɓen na Ekiti ya yi kyau. Mun yi alƙawarin zaɓen Osun zai ma fi kyau, sai ga shi zaɓen na Osun ya yi kyau fiye da wanda ya gabace shi.

“Yanzu mu na maku alƙawarin cewa manyan zaɓuɓɓukan 2023 za su fi duk wani zaɓe da mu ka yi a baya inganci kuma mun sadaukar da kan mu wajen gudanar da zaɓe mafi nagarta.”

Tun da farko, sai da jagoran maziyartan, Mista Frank LaRose, wanda shi ne Sakataren Jihar Ohio ta ƙasar Amurka, ya yaba wa INEC kan ƙoƙarin da ta ke yi na inganta al’amarin zaɓe a Nijeriya.

LaRose, wanda kuma kwamishinan zaɓe ne a Jihar ta Ohio, ya bayyana wannan ziyara da ya fara kawowa a Nijeriya a matsayin wata babbar dama da ya samu ta koyon abubuwa. Ya yi kira ga INEC da ta ci gaba da inganta tsarin zaɓe na Nijeriya.

INEC

Ya ce: “Ina jagorantar maziyarta waɗanda manyan masana ne a harkar zaɓe daga yankin mu, da ma faɗin Amurka.

“Waɗannan maziyartan su na da tunani irin naku na cewa mutanen Nijeriya sun cancanci su ci gaba da samun zaɓe mai inganci babu murɗiya, karɓaɓɓe ga kowa, saboda haka mu na aiki domin shirya wa zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023.

“Mun samu damar kai ziyara a Osun saboda wannan shi ne karo na biyu da aka gudanar da zaɓe a ƙarƙashin sabuwar Dokar Zaɓe.

“Mun haɗu da Kwamishinan Zaɓe Mazaunin can (REC) a Osun kuma mun yi nazarin wuraren kaɗa ƙuri’a daban-daban a Ranar Zaɓe.

“Da farko dai, ina so in yaba wa dukkan ku saboda aikin da ku ke ci gaba da gudanarwa wanda za ku ci gaba da inganta shi. Mun san cewa a ko yaushe akwai buƙatar a inganta aiki.

“Sai dai kuma, akwai buƙatar mu fara da yin la’akari da ingancin da INEC ta ke ta ƙara samu don gudanar da zaɓe mai kyau; kuma wannan wani abu ne da mu ka gani da idanuwan mu, ba wai mun jira wani ya zo ya ba mu labari ba ne.”

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Gidajen Burodi Na Shirin Tsunduma Yajin Aiki

Next Post

Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok A Borno

Related

Somaliya Da ATMIS Sun Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Tsakiyar Kasar
Labarai

Somaliya Da ATMIS Sun Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Tsakiyar Kasar

5 hours ago
Kotu Ta Tabbatar Da Kefas A Matsayin Gwamnan Taraba
Labarai

Kotu Ta Tabbatar Da Kefas A Matsayin Gwamnan Taraba

7 hours ago
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Manyan Labarai

NLC Da TUC Na Hada Kan Ma’aikata Don Tafka Gagarumin Yajin Aiki

7 hours ago
Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya

9 hours ago
Hafsan hafsoshin soji
Labarai

Za Mu Sauya Salon Yaƙi Da Ta’addanci – Hafsan Hafsoshin Soji

10 hours ago
Kotun Zaben Gwamnan Sokoto Ta Kori Karar PDP Ta Tabbatar Da Nasarar Zaben Aliyu
Manyan Labarai

Kotun Zaben Gwamnan Sokoto Ta Kori Karar PDP Ta Tabbatar Da Nasarar Zaben Aliyu

13 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok A Borno

Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin 'Yan Matan Chibok A Borno

LABARAI MASU NASABA

Somaliya Da ATMIS Sun Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Tsakiyar Kasar

Somaliya Da ATMIS Sun Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Tsakiyar Kasar

September 30, 2023
Yadda Aka Samu Jihohi 36 A Nijeriya

Yadda Aka Samu Jihohi 36 A Nijeriya

September 30, 2023
Kotu Ta Tabbatar Da Kefas A Matsayin Gwamnan Taraba

Kotu Ta Tabbatar Da Kefas A Matsayin Gwamnan Taraba

September 30, 2023
’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

September 30, 2023

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Dannau

September 30, 2023
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

NLC Da TUC Na Hada Kan Ma’aikata Don Tafka Gagarumin Yajin Aiki

September 30, 2023
Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

Za A Wallafa Sharhin Xi Kan Ciyar Da Zamanantar Da Kasar Sin Gaba

September 30, 2023
Danbarwar Auren Sadiya Haruna Da G-Fresh Ta Dawo

Danbarwar Auren Sadiya Haruna Da G-Fresh Ta Dawo

September 30, 2023
Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya

Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya

September 30, 2023
AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

AU Ta Yi Kira Da Kara Zurfafa Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Afirka Da Sin

September 30, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.