• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Cike Gurbi: Masu Kada Kuri’a Miliyan 4.5 Za Su Yi Zabe A Fabrairu – INEC

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
katin zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa jimillar ‘yan Nijeriya 4,567,689 za su raba gardama a zaben cike gurbi da zai gudana a watan Fabrairun a jihohi 27.

A cewar sanarwar gabanin zabe da babban sakataren yada labarai na INEC, Mista Rotimi Oyekanmi ya fitar, ta bayyana cewa a cikin adadin, mutum 2,189,171 ne za su raba gardama a zaben cike gurbi a mazabun ‘yan majalisar dattawa guda biyu da kuma mazabu hudu na ‘yan majalisar wakilai da za su gudana a jihohi uku.

  • Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa
  • NERC Ta Kori Dukkan Daraktocin Wutar Lantarki Na Jihar Kaduna 

Sanarwar ta ci gaba da bayyana cewa masu zabe 2,220,912 bisa umurnin kotu za su yi zaben cike gurbi na ‘yan majalisar tarayya, yayin da masu kada kuri’a 157,606 za su gudanar da zaben ‘yan majalisar jihohi.

Zaben cike gurbin zai gudana ne a mazaben ‘yan majalisar dattawa guda biyu a kudancin jihohin Ebony da kuma Yobe ta gabas, yayin da za a gudanar da zaben a mazabu hudu na majalisar wakilai a jihohin Kebbi, Legas, Ondo da Taraba da kuma wasu mazabu uku da ke Benuwai da Borno da Kaduna.

An dai samu wadannan gurbi ne sakamakon ajiye aiki da kuma mutu na wasu ‘yan majalisa.

Labarai Masu Nasaba

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Haka kuma sanarwar ta ce za a gudanar da zaben cike gurbi a mazabar dan majalisa guda daya a Jihar Filato bisa hukuncin kotu da kuma wasu mazabu na tarayya guda 12.

Mazaun ‘yan majalisa da za a gudanar da zaben sun hada da Surulere da ke Jihar Legas, Gauri/Shanta/Ingaski da Arewa/Dandi da suke cikin Jihar Kebbi, Arewa maso gabas da Arewa maso yamma na Akoko da ke Jihar Ondo, Jalingo/Yorro/Zing a Jihar Taraba, Ikono/Ini a Jihar Akwa Ibom da kuma Akamkpa/Biase da ke Jihar Kurus Ribas.

Sauran sun hada da Arewacin Nnewi da Kudancin Nnewi da Arewacin Orumba da kudancin Orumba na Jihar Anambra, Arewacin Igbo Eze da Udenu a Jihar Inugu, Birnin Kudu da Buji da ke Jihar Jigawa, Igabi da Kachiya da Kagarko a Jihar Kaduna, Faskari/Kankara/Sabuwa na Jihar Katsina, Arewacin Jos da Bases a Jihar Filato da kuma Fine da Fune da ke Jihar Yobe.

Haka kuma za a gudanar da zaben ‘yan majalisar dattawa a yammacin Yobe da Filato ta tsakiya bisa hukuncin kotu.

Sannan a matsaki na jiha kuwa, za a gudanar da zaben cike gurbi a jihohin Adamawa, Akwa Ibom Bauchi, Bayelsa, Kurod Ribas, Delta, Inugu, Kaduna, Kano, Nasarawa, Neja, Oyo, Sakwato, Zamfara, Benuwai da kuma Borno.

Za a mika sunayen ‘yan takarar zaben cike gurbi ga hukumar zabe a ranar 13 ga watan Janairu. Sannan za a fitar da sunayen ‘yan takara na karshe a ranar 17 ga Janairu.

Haka kuma za a fara gudanar da kamfen tun daga ranar 18 ga Janairu, sannan za a rufe yakin neman zabe a ranar 1 ga watan Fabrairun 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukuncin ZabeKotun kararrakin zabeRikicin bayan zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gano Dukiyar Iyalan Masarautar Saudiyya Ta Fi Ta Masu Arzikin Duniya Biyu Yawa

Next Post

Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

Related

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
Labarai

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

43 minutes ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

5 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

6 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

6 hours ago
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

7 hours ago
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
Labarai

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

8 hours ago
Next Post
Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

LABARAI MASU NASABA

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

July 4, 2025
Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

July 4, 2025
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.