• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Cike Gurbi: Masu Kada Kuri’a Miliyan 4.5 Za Su Yi Zabe A Fabrairu – INEC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
katin zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa jimillar ‘yan Nijeriya 4,567,689 za su raba gardama a zaben cike gurbi da zai gudana a watan Fabrairun a jihohi 27.

A cewar sanarwar gabanin zabe da babban sakataren yada labarai na INEC, Mista Rotimi Oyekanmi ya fitar, ta bayyana cewa a cikin adadin, mutum 2,189,171 ne za su raba gardama a zaben cike gurbi a mazabun ‘yan majalisar dattawa guda biyu da kuma mazabu hudu na ‘yan majalisar wakilai da za su gudana a jihohi uku.

  • Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa
  • NERC Ta Kori Dukkan Daraktocin Wutar Lantarki Na Jihar Kaduna 

Sanarwar ta ci gaba da bayyana cewa masu zabe 2,220,912 bisa umurnin kotu za su yi zaben cike gurbi na ‘yan majalisar tarayya, yayin da masu kada kuri’a 157,606 za su gudanar da zaben ‘yan majalisar jihohi.

Zaben cike gurbin zai gudana ne a mazaben ‘yan majalisar dattawa guda biyu a kudancin jihohin Ebony da kuma Yobe ta gabas, yayin da za a gudanar da zaben a mazabu hudu na majalisar wakilai a jihohin Kebbi, Legas, Ondo da Taraba da kuma wasu mazabu uku da ke Benuwai da Borno da Kaduna.

An dai samu wadannan gurbi ne sakamakon ajiye aiki da kuma mutu na wasu ‘yan majalisa.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Haka kuma sanarwar ta ce za a gudanar da zaben cike gurbi a mazabar dan majalisa guda daya a Jihar Filato bisa hukuncin kotu da kuma wasu mazabu na tarayya guda 12.

Mazaun ‘yan majalisa da za a gudanar da zaben sun hada da Surulere da ke Jihar Legas, Gauri/Shanta/Ingaski da Arewa/Dandi da suke cikin Jihar Kebbi, Arewa maso gabas da Arewa maso yamma na Akoko da ke Jihar Ondo, Jalingo/Yorro/Zing a Jihar Taraba, Ikono/Ini a Jihar Akwa Ibom da kuma Akamkpa/Biase da ke Jihar Kurus Ribas.

Sauran sun hada da Arewacin Nnewi da Kudancin Nnewi da Arewacin Orumba da kudancin Orumba na Jihar Anambra, Arewacin Igbo Eze da Udenu a Jihar Inugu, Birnin Kudu da Buji da ke Jihar Jigawa, Igabi da Kachiya da Kagarko a Jihar Kaduna, Faskari/Kankara/Sabuwa na Jihar Katsina, Arewacin Jos da Bases a Jihar Filato da kuma Fine da Fune da ke Jihar Yobe.

Haka kuma za a gudanar da zaben ‘yan majalisar dattawa a yammacin Yobe da Filato ta tsakiya bisa hukuncin kotu.

Sannan a matsaki na jiha kuwa, za a gudanar da zaben cike gurbi a jihohin Adamawa, Akwa Ibom Bauchi, Bayelsa, Kurod Ribas, Delta, Inugu, Kaduna, Kano, Nasarawa, Neja, Oyo, Sakwato, Zamfara, Benuwai da kuma Borno.

Za a mika sunayen ‘yan takarar zaben cike gurbi ga hukumar zabe a ranar 13 ga watan Janairu. Sannan za a fitar da sunayen ‘yan takara na karshe a ranar 17 ga Janairu.

Haka kuma za a fara gudanar da kamfen tun daga ranar 18 ga Janairu, sannan za a rufe yakin neman zabe a ranar 1 ga watan Fabrairun 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukuncin ZabeKotun kararrakin zabeRikicin bayan zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gano Dukiyar Iyalan Masarautar Saudiyya Ta Fi Ta Masu Arzikin Duniya Biyu Yawa

Next Post

Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

38 minutes ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

3 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

15 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

16 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

19 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

22 hours ago
Next Post
Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.