ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Cike Gurbi: Masu Kada Kuri’a Miliyan 4.5 Za Su Yi Zabe A Fabrairu – INEC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
katin zabe

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa jimillar ‘yan Nijeriya 4,567,689 za su raba gardama a zaben cike gurbi da zai gudana a watan Fabrairun a jihohi 27.

A cewar sanarwar gabanin zabe da babban sakataren yada labarai na INEC, Mista Rotimi Oyekanmi ya fitar, ta bayyana cewa a cikin adadin, mutum 2,189,171 ne za su raba gardama a zaben cike gurbi a mazabun ‘yan majalisar dattawa guda biyu da kuma mazabu hudu na ‘yan majalisar wakilai da za su gudana a jihohi uku.

  • Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa
  • NERC Ta Kori Dukkan Daraktocin Wutar Lantarki Na Jihar Kaduna 

Sanarwar ta ci gaba da bayyana cewa masu zabe 2,220,912 bisa umurnin kotu za su yi zaben cike gurbi na ‘yan majalisar tarayya, yayin da masu kada kuri’a 157,606 za su gudanar da zaben ‘yan majalisar jihohi.

ADVERTISEMENT

Zaben cike gurbin zai gudana ne a mazaben ‘yan majalisar dattawa guda biyu a kudancin jihohin Ebony da kuma Yobe ta gabas, yayin da za a gudanar da zaben a mazabu hudu na majalisar wakilai a jihohin Kebbi, Legas, Ondo da Taraba da kuma wasu mazabu uku da ke Benuwai da Borno da Kaduna.

An dai samu wadannan gurbi ne sakamakon ajiye aiki da kuma mutu na wasu ‘yan majalisa.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Haka kuma sanarwar ta ce za a gudanar da zaben cike gurbi a mazabar dan majalisa guda daya a Jihar Filato bisa hukuncin kotu da kuma wasu mazabu na tarayya guda 12.

Mazaun ‘yan majalisa da za a gudanar da zaben sun hada da Surulere da ke Jihar Legas, Gauri/Shanta/Ingaski da Arewa/Dandi da suke cikin Jihar Kebbi, Arewa maso gabas da Arewa maso yamma na Akoko da ke Jihar Ondo, Jalingo/Yorro/Zing a Jihar Taraba, Ikono/Ini a Jihar Akwa Ibom da kuma Akamkpa/Biase da ke Jihar Kurus Ribas.

Sauran sun hada da Arewacin Nnewi da Kudancin Nnewi da Arewacin Orumba da kudancin Orumba na Jihar Anambra, Arewacin Igbo Eze da Udenu a Jihar Inugu, Birnin Kudu da Buji da ke Jihar Jigawa, Igabi da Kachiya da Kagarko a Jihar Kaduna, Faskari/Kankara/Sabuwa na Jihar Katsina, Arewacin Jos da Bases a Jihar Filato da kuma Fine da Fune da ke Jihar Yobe.

Haka kuma za a gudanar da zaben ‘yan majalisar dattawa a yammacin Yobe da Filato ta tsakiya bisa hukuncin kotu.

Sannan a matsaki na jiha kuwa, za a gudanar da zaben cike gurbi a jihohin Adamawa, Akwa Ibom Bauchi, Bayelsa, Kurod Ribas, Delta, Inugu, Kaduna, Kano, Nasarawa, Neja, Oyo, Sakwato, Zamfara, Benuwai da kuma Borno.

Za a mika sunayen ‘yan takarar zaben cike gurbi ga hukumar zabe a ranar 13 ga watan Janairu. Sannan za a fitar da sunayen ‘yan takara na karshe a ranar 17 ga Janairu.

Haka kuma za a fara gudanar da kamfen tun daga ranar 18 ga Janairu, sannan za a rufe yakin neman zabe a ranar 1 ga watan Fabrairun 2024.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.