ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Cike Gurbi: Masu Kada Kuri’a Miliyan 4.5 Za Su Yi Zabe A Fabrairu – INEC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
katin zabe

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa jimillar ‘yan Nijeriya 4,567,689 za su raba gardama a zaben cike gurbi da zai gudana a watan Fabrairun a jihohi 27.

A cewar sanarwar gabanin zabe da babban sakataren yada labarai na INEC, Mista Rotimi Oyekanmi ya fitar, ta bayyana cewa a cikin adadin, mutum 2,189,171 ne za su raba gardama a zaben cike gurbi a mazabun ‘yan majalisar dattawa guda biyu da kuma mazabu hudu na ‘yan majalisar wakilai da za su gudana a jihohi uku.

  • Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa
  • NERC Ta Kori Dukkan Daraktocin Wutar Lantarki Na Jihar Kaduna 

Sanarwar ta ci gaba da bayyana cewa masu zabe 2,220,912 bisa umurnin kotu za su yi zaben cike gurbi na ‘yan majalisar tarayya, yayin da masu kada kuri’a 157,606 za su gudanar da zaben ‘yan majalisar jihohi.

ADVERTISEMENT

Zaben cike gurbin zai gudana ne a mazaben ‘yan majalisar dattawa guda biyu a kudancin jihohin Ebony da kuma Yobe ta gabas, yayin da za a gudanar da zaben a mazabu hudu na majalisar wakilai a jihohin Kebbi, Legas, Ondo da Taraba da kuma wasu mazabu uku da ke Benuwai da Borno da Kaduna.

An dai samu wadannan gurbi ne sakamakon ajiye aiki da kuma mutu na wasu ‘yan majalisa.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Haka kuma sanarwar ta ce za a gudanar da zaben cike gurbi a mazabar dan majalisa guda daya a Jihar Filato bisa hukuncin kotu da kuma wasu mazabu na tarayya guda 12.

Mazaun ‘yan majalisa da za a gudanar da zaben sun hada da Surulere da ke Jihar Legas, Gauri/Shanta/Ingaski da Arewa/Dandi da suke cikin Jihar Kebbi, Arewa maso gabas da Arewa maso yamma na Akoko da ke Jihar Ondo, Jalingo/Yorro/Zing a Jihar Taraba, Ikono/Ini a Jihar Akwa Ibom da kuma Akamkpa/Biase da ke Jihar Kurus Ribas.

Sauran sun hada da Arewacin Nnewi da Kudancin Nnewi da Arewacin Orumba da kudancin Orumba na Jihar Anambra, Arewacin Igbo Eze da Udenu a Jihar Inugu, Birnin Kudu da Buji da ke Jihar Jigawa, Igabi da Kachiya da Kagarko a Jihar Kaduna, Faskari/Kankara/Sabuwa na Jihar Katsina, Arewacin Jos da Bases a Jihar Filato da kuma Fine da Fune da ke Jihar Yobe.

Haka kuma za a gudanar da zaben ‘yan majalisar dattawa a yammacin Yobe da Filato ta tsakiya bisa hukuncin kotu.

Sannan a matsaki na jiha kuwa, za a gudanar da zaben cike gurbi a jihohin Adamawa, Akwa Ibom Bauchi, Bayelsa, Kurod Ribas, Delta, Inugu, Kaduna, Kano, Nasarawa, Neja, Oyo, Sakwato, Zamfara, Benuwai da kuma Borno.

Za a mika sunayen ‘yan takarar zaben cike gurbi ga hukumar zabe a ranar 13 ga watan Janairu. Sannan za a fitar da sunayen ‘yan takara na karshe a ranar 17 ga Janairu.

Haka kuma za a fara gudanar da kamfen tun daga ranar 18 ga Janairu, sannan za a rufe yakin neman zabe a ranar 1 ga watan Fabrairun 2024.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Labarai

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Next Post
Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.