• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

byYusuf Shuaibu
1 year ago
Edo

A ranar Asabar din nan ce, mutane a Jihar Edo ke fita rumfunan zabe domin kada kuri’unsu na zaben sabon gwamnan.

Zaben Gwamnan Jihar Edo ya kasance zakaran gwajin dafi da za a fafata a tsakanin manyan jam’iyyun Nijeriya, wanda zaben yake jan hankali a cikin fagen siyasar Nijeriya.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta tsara gudanar da zaben Gwamnan Edo a ranar 21 ga Satumba, 2024.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun hukumar, Sam Olumekun, INEC ta sanya wannan rana domin tabbatar da shirye-shirye da kuma gudanar da zaben cikin lumana.

Ana sa ran masu kada kuri’a a fadin jihar za su fito da yawa domin zaben sabon gwamnan jihar.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Manyan ‘yan takara da za su fafata a wannan zabe sun hada da na jam’iyyar PDP mai mulkin jihar, Asue Ighodal da kuma na jam’iyyar APC, Sanata Monday Okpebholo.

Har ila yau, shi ma dan takarar jam’iyyar LP, Olumide Akpata zai bayar da mamaki a wannan zabe, ganin yadda jam’iyyarsa ta bayar da mamaki a zaben 2023.

Bisa kididdigar da INEC ta fitar na masu rajistar zabe, Jihar Edo na da masu kada kuri’a 2,501,318.

Kwamishiniyar ta Jihar Edo, Farfesa Rhoda Gumus ta sanar da cewa har yanzu masu rajistar zabe 373,030 ne suka kasa karbar katin zabesu a jihar.

Wannan adadi ya nuna yadda al’ummar Edo ke kara wayewa a siyasance, wadanda ke da sha’awar yin amfani da ‘yancinsu na dimokuradiyya.

INEC ta bayyana cewa, masu rajistar zabe guda 2,128,288 ne suka amshi katin zabensu. Wannan lamba wata alama ce mai muhimmanci na shirye-shiryen da masu zabe suke da shi game da zaben Jihar Edo.

Hukumar INEC ta tantance kungiyoyin fararen hula na cikin gida da na kasashen waje wadanda za su sa ido a wannan zabe.

Kungiyoyin dai sun yi kira ga ‘yan takara da magoya bayansu su kai zuciya nesa a lokacin gudanar da zabe domin samun damar yin sahihin zabe a Jihar Edo.

An dai jabge jami’an tsaron tun daga kan ‘yansanda da sojoji da jami’an hukumar farin kaya (DSS) domin jiran ko-ta-kwana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

Yadda Shugabanni Suka Taya Al'ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version