• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Rahotonni
0
Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar din nan ce, mutane a Jihar Edo ke fita rumfunan zabe domin kada kuri’unsu na zaben sabon gwamnan.

Zaben Gwamnan Jihar Edo ya kasance zakaran gwajin dafi da za a fafata a tsakanin manyan jam’iyyun Nijeriya, wanda zaben yake jan hankali a cikin fagen siyasar Nijeriya.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta tsara gudanar da zaben Gwamnan Edo a ranar 21 ga Satumba, 2024.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun hukumar, Sam Olumekun, INEC ta sanya wannan rana domin tabbatar da shirye-shirye da kuma gudanar da zaben cikin lumana.

Ana sa ran masu kada kuri’a a fadin jihar za su fito da yawa domin zaben sabon gwamnan jihar.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Manyan ‘yan takara da za su fafata a wannan zabe sun hada da na jam’iyyar PDP mai mulkin jihar, Asue Ighodal da kuma na jam’iyyar APC, Sanata Monday Okpebholo.

Har ila yau, shi ma dan takarar jam’iyyar LP, Olumide Akpata zai bayar da mamaki a wannan zabe, ganin yadda jam’iyyarsa ta bayar da mamaki a zaben 2023.

Bisa kididdigar da INEC ta fitar na masu rajistar zabe, Jihar Edo na da masu kada kuri’a 2,501,318.

Kwamishiniyar ta Jihar Edo, Farfesa Rhoda Gumus ta sanar da cewa har yanzu masu rajistar zabe 373,030 ne suka kasa karbar katin zabesu a jihar.

Wannan adadi ya nuna yadda al’ummar Edo ke kara wayewa a siyasance, wadanda ke da sha’awar yin amfani da ‘yancinsu na dimokuradiyya.

INEC ta bayyana cewa, masu rajistar zabe guda 2,128,288 ne suka amshi katin zabensu. Wannan lamba wata alama ce mai muhimmanci na shirye-shiryen da masu zabe suke da shi game da zaben Jihar Edo.

Hukumar INEC ta tantance kungiyoyin fararen hula na cikin gida da na kasashen waje wadanda za su sa ido a wannan zabe.

Kungiyoyin dai sun yi kira ga ‘yan takara da magoya bayansu su kai zuciya nesa a lokacin gudanar da zabe domin samun damar yin sahihin zabe a Jihar Edo.

An dai jabge jami’an tsaron tun daga kan ‘yansanda da sojoji da jami’an hukumar farin kaya (DSS) domin jiran ko-ta-kwana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EdoINECZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Edo
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

Yadda Shugabanni Suka Taya Al'ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.