• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

by Yusuf Shuaibu
12 months ago
in Rahotonni
0
Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar din nan ce, mutane a Jihar Edo ke fita rumfunan zabe domin kada kuri’unsu na zaben sabon gwamnan.

Zaben Gwamnan Jihar Edo ya kasance zakaran gwajin dafi da za a fafata a tsakanin manyan jam’iyyun Nijeriya, wanda zaben yake jan hankali a cikin fagen siyasar Nijeriya.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta tsara gudanar da zaben Gwamnan Edo a ranar 21 ga Satumba, 2024.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun hukumar, Sam Olumekun, INEC ta sanya wannan rana domin tabbatar da shirye-shirye da kuma gudanar da zaben cikin lumana.

Ana sa ran masu kada kuri’a a fadin jihar za su fito da yawa domin zaben sabon gwamnan jihar.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Manyan ‘yan takara da za su fafata a wannan zabe sun hada da na jam’iyyar PDP mai mulkin jihar, Asue Ighodal da kuma na jam’iyyar APC, Sanata Monday Okpebholo.

Har ila yau, shi ma dan takarar jam’iyyar LP, Olumide Akpata zai bayar da mamaki a wannan zabe, ganin yadda jam’iyyarsa ta bayar da mamaki a zaben 2023.

Bisa kididdigar da INEC ta fitar na masu rajistar zabe, Jihar Edo na da masu kada kuri’a 2,501,318.

Kwamishiniyar ta Jihar Edo, Farfesa Rhoda Gumus ta sanar da cewa har yanzu masu rajistar zabe 373,030 ne suka kasa karbar katin zabesu a jihar.

Wannan adadi ya nuna yadda al’ummar Edo ke kara wayewa a siyasance, wadanda ke da sha’awar yin amfani da ‘yancinsu na dimokuradiyya.

INEC ta bayyana cewa, masu rajistar zabe guda 2,128,288 ne suka amshi katin zabensu. Wannan lamba wata alama ce mai muhimmanci na shirye-shiryen da masu zabe suke da shi game da zaben Jihar Edo.

Hukumar INEC ta tantance kungiyoyin fararen hula na cikin gida da na kasashen waje wadanda za su sa ido a wannan zabe.

Kungiyoyin dai sun yi kira ga ‘yan takara da magoya bayansu su kai zuciya nesa a lokacin gudanar da zabe domin samun damar yin sahihin zabe a Jihar Edo.

An dai jabge jami’an tsaron tun daga kan ‘yansanda da sojoji da jami’an hukumar farin kaya (DSS) domin jiran ko-ta-kwana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EdoINECZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

5 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

1 week ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

Yadda Shugabanni Suka Taya Al'ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.