• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Edo

A ranar Asabar din nan ce, mutane a Jihar Edo ke fita rumfunan zabe domin kada kuri’unsu na zaben sabon gwamnan.

Zaben Gwamnan Jihar Edo ya kasance zakaran gwajin dafi da za a fafata a tsakanin manyan jam’iyyun Nijeriya, wanda zaben yake jan hankali a cikin fagen siyasar Nijeriya.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta tsara gudanar da zaben Gwamnan Edo a ranar 21 ga Satumba, 2024.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun hukumar, Sam Olumekun, INEC ta sanya wannan rana domin tabbatar da shirye-shirye da kuma gudanar da zaben cikin lumana.

Ana sa ran masu kada kuri’a a fadin jihar za su fito da yawa domin zaben sabon gwamnan jihar.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Manyan ‘yan takara da za su fafata a wannan zabe sun hada da na jam’iyyar PDP mai mulkin jihar, Asue Ighodal da kuma na jam’iyyar APC, Sanata Monday Okpebholo.

Har ila yau, shi ma dan takarar jam’iyyar LP, Olumide Akpata zai bayar da mamaki a wannan zabe, ganin yadda jam’iyyarsa ta bayar da mamaki a zaben 2023.

Bisa kididdigar da INEC ta fitar na masu rajistar zabe, Jihar Edo na da masu kada kuri’a 2,501,318.

Kwamishiniyar ta Jihar Edo, Farfesa Rhoda Gumus ta sanar da cewa har yanzu masu rajistar zabe 373,030 ne suka kasa karbar katin zabesu a jihar.

Wannan adadi ya nuna yadda al’ummar Edo ke kara wayewa a siyasance, wadanda ke da sha’awar yin amfani da ‘yancinsu na dimokuradiyya.

INEC ta bayyana cewa, masu rajistar zabe guda 2,128,288 ne suka amshi katin zabensu. Wannan lamba wata alama ce mai muhimmanci na shirye-shiryen da masu zabe suke da shi game da zaben Jihar Edo.

Hukumar INEC ta tantance kungiyoyin fararen hula na cikin gida da na kasashen waje wadanda za su sa ido a wannan zabe.

Kungiyoyin dai sun yi kira ga ‘yan takara da magoya bayansu su kai zuciya nesa a lokacin gudanar da zabe domin samun damar yin sahihin zabe a Jihar Edo.

An dai jabge jami’an tsaron tun daga kan ‘yansanda da sojoji da jami’an hukumar farin kaya (DSS) domin jiran ko-ta-kwana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Yadda Shugabanni Suka Taya Al’ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

Yadda Shugabanni Suka Taya Al'ummar Musulmi Murnar Maulidin Bana

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.