Mai shari’a Inyang Ekwo na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, ya yi watsi da karar da Sanata Aisha Dahiru Ahmed Binani, ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar Adamawa ta shigar a 2023.
Sanata Binani ta garzaya kotu ne domin neman a sake duba hukuncin da hukumar zabe ta kasa (INEC) ta yanke na sauya ta a matsayin wacce ta lashe zaben gwamna kamar yadda kwamishinan zabe na jihar, Hudu Yunusa-Ari ya bayyana.
A yayin zaman da aka yi a ranar Laraba, Lauyan Sanata Binani ya shaida wa Kotun cewa tuni ya ya rubuta sanarwa kan dakatar da karar da ya shigar kamar yadda mai karar ta umarta.
Don haka ya roki kotun da ta yi watsi da karar.
Shima a hukuncin da ya yanke, alkalin kotun, Mai shari’a Inyang Ekwo ya zabi ya yi watsi da karar kuma ya yi watsi da karar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp