• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa: Hukuncin Kotu Da Rikice-rikice Na Matukar Kawo Mana Cikas A Shirye-shiryenmu —INEC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa hukuncin kotu kan ‘yan takara da rikice-rikicen da ke faruwa a jihohin suna matukar kawo mana cikas game da shirye-shiryen hukumar na gudanar da sahihin zabe a ranar 11 ga Nuwambar 2023.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ya bayyana hakan a wani taro tare da jam’iyyun siyasa wanda ya gudana a Abuja.

  • Gobe Za A Tsame Duk Ma’aikacin Tarayya Da Ba Ya Cikin Tsarin IPPIS Daga Biyan Albashi
  • Gwamnatin Tinubu Za Ta Muhimmanta Amfani Da Na’urorin Zamani A Gidajen Rediyo Da Talabijin – Minista

Ya nuna matukar damuwarsa game da rikice-rikicen da suke tasowa a wadannan jihohi guda uku a tsakanin magoya bayan jam’iyya da ‘yan takara, ya yi gargadin cewa babu yadda za a yi a iya gudanar da sahihin zabe babu cikakken zaman lafiya.

“Sake buga kayayyaki zabe bisa bin umarnin hukuncin kotu cikin kankanin lokaci ba wai tsada ba ne kawai har ma yana shafar ayyukan hukumar. Ko da yake hukumar ta riga ta fitar da jerin sunayen ‘yan takarar jihohin uku, amma umarnin kotu guda hudu da ya tilasta mana sake duba jerin sunayen.

“Wadannan canje-canjen sun bayyana a cikin sabunta jerin jam’iyyu da ‘yan takara a shafinmu na sada zumunta. Daukar wannan hukuncin ba tare da la’akari da abin da zai janyo ya shafi hukumar da ‘yan takarar ko jam’iyyunsu.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

“Yayin da yakin neman zabe ke ci gaba da dagula lamura, hukumar ta sake jaddada damuwarta game da yawaitar tashe-tashen hankula a jihohin uku da suka hada da jam’iyyu da ‘yan takara. Ina so in tunatar da ku a matsayinku na shugabannin jam’iyya cewa zabuka na gaskiya da adalci ba zai yiwu ba sai cikin yanayi na zaman lafiya,” in ji Yakubu.

Shugaban INEC ya ce zaben wani tsari ne da ya kunshi Bil’adama a matsayin masu jefa kuri’a, masu sa ido da kuma kafafen yada labarai wadanda tsaron lafiyarsu ya shafi hukumar.

Yakubu ya ce zabukan a jihohin guda uku yana da matukar rudani a wajen gudanarwa.

Ya kara da cewa a daidai lokacin da ya rage makwanni biyu kacal a gudanar da zaben, INEC na gab da kammala shirye-shiryenta kuma wannan shi ne karo na farko da hukumar za ta gudanar da zabukan gwamnoni guda uku a lokaci guda a yankuna daban-daban.

“Hakan zai yiwu ne a daidai lokacin da masu rike da mukaman suke cika wa’adin mulkisu wanda bai wuce kwanaki 150 ba ko kuma bayan kwanaki 30 kafin cikar wa’adin mulkinsu a gudanar da zabe kamar yadda sashe na 178 (2) na kunkundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 ya tanada,” in ji shi.

Da yake mayar da martani a madadin jam’iyyun siyasar da suka yi rajista, shugaban kungiyar IPAC, Injiniya Yabagi Sani, ya ce domin tabbatar da amincewar ‘yan kasa, dole ne INEC ta ci gaba da nuna rashin son kai da gaskiya da kuma jajircewa wajen gudanar da sahihin zabe na gaskiya da adalci.

Ya kuma bukaci INEC da ta yi aiki tukuru tare da hada kai da jami’an tsaro wajen dakile matsalar tsaro da ‘yan siyasa masu daukar siyasa a mutu ko a yi rai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Hon. Dasuki

Next Post

Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

2 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

4 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.