ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa: Hukuncin Kotu Da Rikice-rikice Na Matukar Kawo Mana Cikas A Shirye-shiryenmu —INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
kOgi

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa hukuncin kotu kan ‘yan takara da rikice-rikicen da ke faruwa a jihohin suna matukar kawo mana cikas game da shirye-shiryen hukumar na gudanar da sahihin zabe a ranar 11 ga Nuwambar 2023.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ya bayyana hakan a wani taro tare da jam’iyyun siyasa wanda ya gudana a Abuja.

  • Gobe Za A Tsame Duk Ma’aikacin Tarayya Da Ba Ya Cikin Tsarin IPPIS Daga Biyan Albashi
  • Gwamnatin Tinubu Za Ta Muhimmanta Amfani Da Na’urorin Zamani A Gidajen Rediyo Da Talabijin – Minista

Ya nuna matukar damuwarsa game da rikice-rikicen da suke tasowa a wadannan jihohi guda uku a tsakanin magoya bayan jam’iyya da ‘yan takara, ya yi gargadin cewa babu yadda za a yi a iya gudanar da sahihin zabe babu cikakken zaman lafiya.

ADVERTISEMENT

“Sake buga kayayyaki zabe bisa bin umarnin hukuncin kotu cikin kankanin lokaci ba wai tsada ba ne kawai har ma yana shafar ayyukan hukumar. Ko da yake hukumar ta riga ta fitar da jerin sunayen ‘yan takarar jihohin uku, amma umarnin kotu guda hudu da ya tilasta mana sake duba jerin sunayen.

“Wadannan canje-canjen sun bayyana a cikin sabunta jerin jam’iyyu da ‘yan takara a shafinmu na sada zumunta. Daukar wannan hukuncin ba tare da la’akari da abin da zai janyo ya shafi hukumar da ‘yan takarar ko jam’iyyunsu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Yayin da yakin neman zabe ke ci gaba da dagula lamura, hukumar ta sake jaddada damuwarta game da yawaitar tashe-tashen hankula a jihohin uku da suka hada da jam’iyyu da ‘yan takara. Ina so in tunatar da ku a matsayinku na shugabannin jam’iyya cewa zabuka na gaskiya da adalci ba zai yiwu ba sai cikin yanayi na zaman lafiya,” in ji Yakubu.

Shugaban INEC ya ce zaben wani tsari ne da ya kunshi Bil’adama a matsayin masu jefa kuri’a, masu sa ido da kuma kafafen yada labarai wadanda tsaron lafiyarsu ya shafi hukumar.

Yakubu ya ce zabukan a jihohin guda uku yana da matukar rudani a wajen gudanarwa.

Ya kara da cewa a daidai lokacin da ya rage makwanni biyu kacal a gudanar da zaben, INEC na gab da kammala shirye-shiryenta kuma wannan shi ne karo na farko da hukumar za ta gudanar da zabukan gwamnoni guda uku a lokaci guda a yankuna daban-daban.

“Hakan zai yiwu ne a daidai lokacin da masu rike da mukaman suke cika wa’adin mulkisu wanda bai wuce kwanaki 150 ba ko kuma bayan kwanaki 30 kafin cikar wa’adin mulkinsu a gudanar da zabe kamar yadda sashe na 178 (2) na kunkundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 ya tanada,” in ji shi.

Da yake mayar da martani a madadin jam’iyyun siyasar da suka yi rajista, shugaban kungiyar IPAC, Injiniya Yabagi Sani, ya ce domin tabbatar da amincewar ‘yan kasa, dole ne INEC ta ci gaba da nuna rashin son kai da gaskiya da kuma jajircewa wajen gudanar da sahihin zabe na gaskiya da adalci.

Ya kuma bukaci INEC da ta yi aiki tukuru tare da hada kai da jami’an tsaro wajen dakile matsalar tsaro da ‘yan siyasa masu daukar siyasa a mutu ko a yi rai.

kOgi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

kOgi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.