• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Jihar Zamfara: Zafin Kaye Ya Sa Gwamna Matawalle Sunbatu A Kan Sojoji

by Bello Hamza
3 years ago
Zamfara

A tattauanwarsa da sashin Hausa na gidan radiyon DW, Gwamnan Jihar Zamfara mai barin gado, Bello Mohammed Matawalle, ya yi wata magana mai ban mamaki a kan dalilan da suka sanya ya fadi zaben neman sake mulkin Jihar a karo na biyu, yana ma dora alhakin haka a kan wai taron dangin da sojoji Nijeriya suka yi masa, inda wai suka hada karfi don kayar da shi a zaben da aka yi.

Kayar da Matawalle na daya daga cikin manya-mayan abubunwa bazata da sukia bayar da mamaki a zaben shekarar 2023. Ya sha kayen ne a hannun tsohon ma’aikacin banki wanda ‘yan jam’iyyar APC ke yi wa shaguben cewa, ba kwararren dan siyasa ba ne, wai mutum ne da bashi da kwarewar da zai iya cin zaben ko na karamar hukuma, amma sai gashi mutumin da ke yi wa kallon bashi da kwarewa ya lashe zabe, hukumar zabe INEC ta sanar da shi a matsayin gwamna mai jiran gado a Jihar Zamfara.

  • Ce-ce-ce-kucen Kafa Gwamnatin Rikon Kwarya: Dimbin Tambayoyin Da Aka Kasa Amsawa Har Yanzu

Abin da ya faru a Jihar Zamfara, wani taron dangi ne na tsofaffin gwamnoni 3 da manya-manyan ‘yan siyasar jihar masu ji da kansu, suka tararwa sabon dan siyasa da ya shigo fagen siyasa a shekarar 2018, tabbas wannan wani babban lamari ne a siyasance da a halin yanzu ya shiga kudin tarihin siyasar Jihar Zamfara kuma ba za a mance da shi ba a cikin gaggawa.

Matawalle da jam’iyyar APC sun yi duk kokarin da za su iya yi don daburta tsarin zaben, tun daga tayar da hankula a cibiyoyin zabe da kuma kokarin canza alkalumman zaben daga cibiyoyn zabe, mazabu da kanananan hukumomi.

Wannan fa shi ne dai Matawalle da ake zargin ya yin garkuwa da babban jami’in zaben garinsu na karamar hukumar Maradun inda ya nemi ya sake rubuta sakamakon zabe tare da yi masa ariginzon kuri’u, amma godiya ga na’urar BBAS da ‘IRev portal’ da suka sanya aikin da suka yi ya zaman a banza.

LABARAI MASU NASABA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Yana da matukar wahala, babban jami’in tsaron jihar da harkokin ‘yan ta’adda suya addabe ta ya fito fili ya mai cewa wai an samar da sojoji 50 don kare kowacce rumfar zabe a fadin jihar. Wannan bayanin kadai ya isa ya karfafa al’umma Jihar Zamfara su yi watsi da Matawalle.

Domin kuwa hakan yana nuna cewa, lallai ya jahilci yadda ake tafiyar da harkokin tsaro a kasar nan, ciki kuwa har da yawan jami’an da ake da su a dukkan bangarorin rundunonin tsaron Nijeriya.

Jihar Zamfara na da kimanin runfunan zabe 3,529. Bamu san inda Gwamna ya koyo darasin lissafinsa ba, amma ko ma wanene ya koya masa lissafi lallai gagarabadau ne, don inda ka lissafa sojoji 50 sau yawan funfunan zabe 3,529, zaka samu 176, 450.

A ta bakin Gwamna Matawalle, kenan an turo sojoji 176, 450 don yin aikin zabe a Jihar Zamfara. Shin mu gaya masa gaskiya ko kuma mu bari gaskiyar ta tayar da shi daga barcin da yake yi? Babban abin da ya rage masa shi ne ya natsu ya mutumta ra’ayin al’ujmmar jihar Zamfara, ya kuma mutunta kansa ta hanyar yin ritaya daga harkokin siyasa ta yadda zai tsira daga abubuwan da za su kunyata shi.

Rundunar sojojin Nijeriya nada dakaru 230, 000, amma abin da Gwamna Matawalle ke kokarin bayyana wa al’umma shi ne dakaru 53,550 cikin sojojin Nijeriya aka tura sauran jihohin Nijeriya don kula da yadda aka yi zaben Gwamna, sauran dakaru 176, 450 kuma aka tura su Jihar Zamfara.

Adaidai wannan lokacin yana da matukar wahala wani mai cikakken hankali ya fahimci hikimar da ke tattare da abin da Matawalle ke kokarin bayyanawa don dukkan maganganunsa sun yi karo da duk wata tunani na hankali da za a iya fahimta. Duk da cewa, a lokutta da dama ya sha nuna yadda baya lissafi da tunani kafin ya furta wasu maganganunsa.

Muna kawar da fuska daga maganganun Gwamnan da ya yi imanin sauya sheka zuwa jam’iyya mai mulki ta APC zai iya bashi nasarar darewa karagar mulki karo na biyu ba tare da wata mastsala ba. Tabbas yana nan yana cikin jimami da mamakin yadda lamarin kayensa ya faru. Duk da haka kuma ba za mu aminta da wasu maganganun da za su nemi jirkita gaskiya ba.

Babu gaskiya a maganganun Matawalle. Ko yaro dan makarantar firamare ba zai aminta da wannan maganganu na sa ba. Gwamnan na nema madafa ne kawai don a tausaya masa. Yana kokarin ya nuna kamar ba wai al’umma jihar suka yi watsi da shi suka kuma yi waje rod da shi ba saboda rashin iya aiki.
Jajirtattun al’umma Jihar Zamfara sun toshe duk wata kofa na magudi, basu samu abin da suka saba yi ba a ranakun zabe.

Tabbas, dinbin matasan Jihar Zamfara wadanda suka gaji da salon mulkin Matawalle suka yi sanadiyyar faduwarsa, ‘yan fanshon da aka kwashe kudaden su na cikin dalilan da suka haifar da faduwar Matawalle.

Banda ma haka, abin nda ya faru da Matawalle lamari ne daga Allah, idan za a iya tunawa, an ji shi a wani faifai bidiyo yana cewa, “In har na ci amanar PDP, kada Allah ya ba ni zaman lafiya har karshen rayuwata, na rantse da Allah. In har zan bar PDP ko in cuci mambobinta, Allah ya tsine mini”.

A takaita surutu Gawmna. Lokaci ne na yin tunani tare da tuba. Lokaci ne na sabon shafi ga Jihar Zamfara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post

Kungiyar Mawallafa Labarai Ta Zariya Ta Mika Ta’aziyyarta Ga Editan LEADERSHIP Bisa Rasuwar Mahaifinsa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

October 22, 2025
Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

October 22, 2025
Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

October 22, 2025
Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.