ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Jihar Zamfara: Zafin Kaye Ya Sa Gwamna Matawalle Sunbatu A Kan Sojoji

by Bello Hamza
3 years ago
Zamfara

A tattauanwarsa da sashin Hausa na gidan radiyon DW, Gwamnan Jihar Zamfara mai barin gado, Bello Mohammed Matawalle, ya yi wata magana mai ban mamaki a kan dalilan da suka sanya ya fadi zaben neman sake mulkin Jihar a karo na biyu, yana ma dora alhakin haka a kan wai taron dangin da sojoji Nijeriya suka yi masa, inda wai suka hada karfi don kayar da shi a zaben da aka yi.

Kayar da Matawalle na daya daga cikin manya-mayan abubunwa bazata da sukia bayar da mamaki a zaben shekarar 2023. Ya sha kayen ne a hannun tsohon ma’aikacin banki wanda ‘yan jam’iyyar APC ke yi wa shaguben cewa, ba kwararren dan siyasa ba ne, wai mutum ne da bashi da kwarewar da zai iya cin zaben ko na karamar hukuma, amma sai gashi mutumin da ke yi wa kallon bashi da kwarewa ya lashe zabe, hukumar zabe INEC ta sanar da shi a matsayin gwamna mai jiran gado a Jihar Zamfara.

  • Ce-ce-ce-kucen Kafa Gwamnatin Rikon Kwarya: Dimbin Tambayoyin Da Aka Kasa Amsawa Har Yanzu

Abin da ya faru a Jihar Zamfara, wani taron dangi ne na tsofaffin gwamnoni 3 da manya-manyan ‘yan siyasar jihar masu ji da kansu, suka tararwa sabon dan siyasa da ya shigo fagen siyasa a shekarar 2018, tabbas wannan wani babban lamari ne a siyasance da a halin yanzu ya shiga kudin tarihin siyasar Jihar Zamfara kuma ba za a mance da shi ba a cikin gaggawa.

ADVERTISEMENT

Matawalle da jam’iyyar APC sun yi duk kokarin da za su iya yi don daburta tsarin zaben, tun daga tayar da hankula a cibiyoyin zabe da kuma kokarin canza alkalumman zaben daga cibiyoyn zabe, mazabu da kanananan hukumomi.

Wannan fa shi ne dai Matawalle da ake zargin ya yin garkuwa da babban jami’in zaben garinsu na karamar hukumar Maradun inda ya nemi ya sake rubuta sakamakon zabe tare da yi masa ariginzon kuri’u, amma godiya ga na’urar BBAS da ‘IRev portal’ da suka sanya aikin da suka yi ya zaman a banza.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Yana da matukar wahala, babban jami’in tsaron jihar da harkokin ‘yan ta’adda suya addabe ta ya fito fili ya mai cewa wai an samar da sojoji 50 don kare kowacce rumfar zabe a fadin jihar. Wannan bayanin kadai ya isa ya karfafa al’umma Jihar Zamfara su yi watsi da Matawalle.

Domin kuwa hakan yana nuna cewa, lallai ya jahilci yadda ake tafiyar da harkokin tsaro a kasar nan, ciki kuwa har da yawan jami’an da ake da su a dukkan bangarorin rundunonin tsaron Nijeriya.

Jihar Zamfara na da kimanin runfunan zabe 3,529. Bamu san inda Gwamna ya koyo darasin lissafinsa ba, amma ko ma wanene ya koya masa lissafi lallai gagarabadau ne, don inda ka lissafa sojoji 50 sau yawan funfunan zabe 3,529, zaka samu 176, 450.

A ta bakin Gwamna Matawalle, kenan an turo sojoji 176, 450 don yin aikin zabe a Jihar Zamfara. Shin mu gaya masa gaskiya ko kuma mu bari gaskiyar ta tayar da shi daga barcin da yake yi? Babban abin da ya rage masa shi ne ya natsu ya mutumta ra’ayin al’ujmmar jihar Zamfara, ya kuma mutunta kansa ta hanyar yin ritaya daga harkokin siyasa ta yadda zai tsira daga abubuwan da za su kunyata shi.

Rundunar sojojin Nijeriya nada dakaru 230, 000, amma abin da Gwamna Matawalle ke kokarin bayyana wa al’umma shi ne dakaru 53,550 cikin sojojin Nijeriya aka tura sauran jihohin Nijeriya don kula da yadda aka yi zaben Gwamna, sauran dakaru 176, 450 kuma aka tura su Jihar Zamfara.

Adaidai wannan lokacin yana da matukar wahala wani mai cikakken hankali ya fahimci hikimar da ke tattare da abin da Matawalle ke kokarin bayyanawa don dukkan maganganunsa sun yi karo da duk wata tunani na hankali da za a iya fahimta. Duk da cewa, a lokutta da dama ya sha nuna yadda baya lissafi da tunani kafin ya furta wasu maganganunsa.

Muna kawar da fuska daga maganganun Gwamnan da ya yi imanin sauya sheka zuwa jam’iyya mai mulki ta APC zai iya bashi nasarar darewa karagar mulki karo na biyu ba tare da wata mastsala ba. Tabbas yana nan yana cikin jimami da mamakin yadda lamarin kayensa ya faru. Duk da haka kuma ba za mu aminta da wasu maganganun da za su nemi jirkita gaskiya ba.

Babu gaskiya a maganganun Matawalle. Ko yaro dan makarantar firamare ba zai aminta da wannan maganganu na sa ba. Gwamnan na nema madafa ne kawai don a tausaya masa. Yana kokarin ya nuna kamar ba wai al’umma jihar suka yi watsi da shi suka kuma yi waje rod da shi ba saboda rashin iya aiki.
Jajirtattun al’umma Jihar Zamfara sun toshe duk wata kofa na magudi, basu samu abin da suka saba yi ba a ranakun zabe.

Tabbas, dinbin matasan Jihar Zamfara wadanda suka gaji da salon mulkin Matawalle suka yi sanadiyyar faduwarsa, ‘yan fanshon da aka kwashe kudaden su na cikin dalilan da suka haifar da faduwar Matawalle.

Banda ma haka, abin nda ya faru da Matawalle lamari ne daga Allah, idan za a iya tunawa, an ji shi a wani faifai bidiyo yana cewa, “In har na ci amanar PDP, kada Allah ya ba ni zaman lafiya har karshen rayuwata, na rantse da Allah. In har zan bar PDP ko in cuci mambobinta, Allah ya tsine mini”.

A takaita surutu Gawmna. Lokaci ne na yin tunani tare da tuba. Lokaci ne na sabon shafi ga Jihar Zamfara.

Zamfara
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post

Kungiyar Mawallafa Labarai Ta Zariya Ta Mika Ta’aziyyarta Ga Editan LEADERSHIP Bisa Rasuwar Mahaifinsa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.