ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Jihar Zamfara: Zafin Kaye Ya Sa Gwamna Matawalle Sunbatu A Kan Sojoji

by Bello Hamza
3 years ago
Zamfara

A tattauanwarsa da sashin Hausa na gidan radiyon DW, Gwamnan Jihar Zamfara mai barin gado, Bello Mohammed Matawalle, ya yi wata magana mai ban mamaki a kan dalilan da suka sanya ya fadi zaben neman sake mulkin Jihar a karo na biyu, yana ma dora alhakin haka a kan wai taron dangin da sojoji Nijeriya suka yi masa, inda wai suka hada karfi don kayar da shi a zaben da aka yi.

Kayar da Matawalle na daya daga cikin manya-mayan abubunwa bazata da sukia bayar da mamaki a zaben shekarar 2023. Ya sha kayen ne a hannun tsohon ma’aikacin banki wanda ‘yan jam’iyyar APC ke yi wa shaguben cewa, ba kwararren dan siyasa ba ne, wai mutum ne da bashi da kwarewar da zai iya cin zaben ko na karamar hukuma, amma sai gashi mutumin da ke yi wa kallon bashi da kwarewa ya lashe zabe, hukumar zabe INEC ta sanar da shi a matsayin gwamna mai jiran gado a Jihar Zamfara.

  • Ce-ce-ce-kucen Kafa Gwamnatin Rikon Kwarya: Dimbin Tambayoyin Da Aka Kasa Amsawa Har Yanzu

Abin da ya faru a Jihar Zamfara, wani taron dangi ne na tsofaffin gwamnoni 3 da manya-manyan ‘yan siyasar jihar masu ji da kansu, suka tararwa sabon dan siyasa da ya shigo fagen siyasa a shekarar 2018, tabbas wannan wani babban lamari ne a siyasance da a halin yanzu ya shiga kudin tarihin siyasar Jihar Zamfara kuma ba za a mance da shi ba a cikin gaggawa.

ADVERTISEMENT

Matawalle da jam’iyyar APC sun yi duk kokarin da za su iya yi don daburta tsarin zaben, tun daga tayar da hankula a cibiyoyin zabe da kuma kokarin canza alkalumman zaben daga cibiyoyn zabe, mazabu da kanananan hukumomi.

Wannan fa shi ne dai Matawalle da ake zargin ya yin garkuwa da babban jami’in zaben garinsu na karamar hukumar Maradun inda ya nemi ya sake rubuta sakamakon zabe tare da yi masa ariginzon kuri’u, amma godiya ga na’urar BBAS da ‘IRev portal’ da suka sanya aikin da suka yi ya zaman a banza.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Yana da matukar wahala, babban jami’in tsaron jihar da harkokin ‘yan ta’adda suya addabe ta ya fito fili ya mai cewa wai an samar da sojoji 50 don kare kowacce rumfar zabe a fadin jihar. Wannan bayanin kadai ya isa ya karfafa al’umma Jihar Zamfara su yi watsi da Matawalle.

Domin kuwa hakan yana nuna cewa, lallai ya jahilci yadda ake tafiyar da harkokin tsaro a kasar nan, ciki kuwa har da yawan jami’an da ake da su a dukkan bangarorin rundunonin tsaron Nijeriya.

Jihar Zamfara na da kimanin runfunan zabe 3,529. Bamu san inda Gwamna ya koyo darasin lissafinsa ba, amma ko ma wanene ya koya masa lissafi lallai gagarabadau ne, don inda ka lissafa sojoji 50 sau yawan funfunan zabe 3,529, zaka samu 176, 450.

A ta bakin Gwamna Matawalle, kenan an turo sojoji 176, 450 don yin aikin zabe a Jihar Zamfara. Shin mu gaya masa gaskiya ko kuma mu bari gaskiyar ta tayar da shi daga barcin da yake yi? Babban abin da ya rage masa shi ne ya natsu ya mutumta ra’ayin al’ujmmar jihar Zamfara, ya kuma mutunta kansa ta hanyar yin ritaya daga harkokin siyasa ta yadda zai tsira daga abubuwan da za su kunyata shi.

Rundunar sojojin Nijeriya nada dakaru 230, 000, amma abin da Gwamna Matawalle ke kokarin bayyana wa al’umma shi ne dakaru 53,550 cikin sojojin Nijeriya aka tura sauran jihohin Nijeriya don kula da yadda aka yi zaben Gwamna, sauran dakaru 176, 450 kuma aka tura su Jihar Zamfara.

Adaidai wannan lokacin yana da matukar wahala wani mai cikakken hankali ya fahimci hikimar da ke tattare da abin da Matawalle ke kokarin bayyanawa don dukkan maganganunsa sun yi karo da duk wata tunani na hankali da za a iya fahimta. Duk da cewa, a lokutta da dama ya sha nuna yadda baya lissafi da tunani kafin ya furta wasu maganganunsa.

Muna kawar da fuska daga maganganun Gwamnan da ya yi imanin sauya sheka zuwa jam’iyya mai mulki ta APC zai iya bashi nasarar darewa karagar mulki karo na biyu ba tare da wata mastsala ba. Tabbas yana nan yana cikin jimami da mamakin yadda lamarin kayensa ya faru. Duk da haka kuma ba za mu aminta da wasu maganganun da za su nemi jirkita gaskiya ba.

Babu gaskiya a maganganun Matawalle. Ko yaro dan makarantar firamare ba zai aminta da wannan maganganu na sa ba. Gwamnan na nema madafa ne kawai don a tausaya masa. Yana kokarin ya nuna kamar ba wai al’umma jihar suka yi watsi da shi suka kuma yi waje rod da shi ba saboda rashin iya aiki.
Jajirtattun al’umma Jihar Zamfara sun toshe duk wata kofa na magudi, basu samu abin da suka saba yi ba a ranakun zabe.

Tabbas, dinbin matasan Jihar Zamfara wadanda suka gaji da salon mulkin Matawalle suka yi sanadiyyar faduwarsa, ‘yan fanshon da aka kwashe kudaden su na cikin dalilan da suka haifar da faduwar Matawalle.

Banda ma haka, abin nda ya faru da Matawalle lamari ne daga Allah, idan za a iya tunawa, an ji shi a wani faifai bidiyo yana cewa, “In har na ci amanar PDP, kada Allah ya ba ni zaman lafiya har karshen rayuwata, na rantse da Allah. In har zan bar PDP ko in cuci mambobinta, Allah ya tsine mini”.

A takaita surutu Gawmna. Lokaci ne na yin tunani tare da tuba. Lokaci ne na sabon shafi ga Jihar Zamfara.

Zamfara
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post

Kungiyar Mawallafa Labarai Ta Zariya Ta Mika Ta’aziyyarta Ga Editan LEADERSHIP Bisa Rasuwar Mahaifinsa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.