ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kano: Alkali Na Fuskantar Tuhuma Kan Kuskuren Da Aka Tafka

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Kano

Yayin da jama’a ke nuna rashin jin dadinsu kan hukuncin da wasu alkalan kotunan daukaka kara suka yi a kan zaben Gwamnan Jihar Kano, majalisar kula da shari’a ta kasa (NJC) ta fara daukan matakai kan wannan lamarin.

Na farko daga cikin alkalan da suke fuskantar tuhuma daga NJC shi ne, mai shari’a Moore Aseimo Abraham Adumein na kotun daukaka kara wanda ya zartar da hukunci mai cike da ce-ce-ku-ce a shari’ar gwamnan Jihar Kano.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Kwamitin Mutum 8 Don Inganta Harkokin Aikin Hajjin 2024
  • Da Dumi-dumi: Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Kujerar Gwamnan Adamawa

LEADERSHIP ta ruwaito cewa mai shari’a Adumein yana fuskantar tuhuma saboda gazawarsa wajen ganowa da kuma kyara kura-kuran rubutun da aka yi a shari’ar Gwamnan Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Wata majiyar ta ce da yawa daga cikin ‘yan Nijeriya sun yi korafi kan hukuncin shara’ar gwamnan Kano, wanda har yanzu suke bukatar yi musu bayanin yadda aka samu kura-kuran.

“Yawancin ‘yan Nijeriya da ke magana a kan hukuncin ba su karanta ba. Kuskuren da aka samu a hukuncin ya nuna karara kuskure ne na alkali amma ba na yi masa uzuri ba, dole ne ya amsa kuskurensa saboda jahilci ba uzuri ba ne a shari’a, dole ne ya fuskanci hukunci a wuyansa.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

“Kuskuren wannan hukuncin ya fito ne daga magatakarda wanda ya yi aiki a kai. Alkalin bai karanta karshen hukuncin ba bayan da sakatare ya yi aiki a kai. Alkalin da sakataren da suka yi aiki a kai dole ne su fuskanci hukunci,” in ji majiyar.

Majiyar ta ci gaba da cewa a bangaren shari’a tafka kuskure babban abin kunya ne ba kamar sauran sass aba, shi ya sa kuskure ke zama babban laifi idan an aikata a bangaren.

Ya ce NJC ba ta kare alkalan ta da aka samu da laifin ko kuma kuskure wajen gudanar da aiki. Majiyar ta ce, “Kusan kashi 98 cikin 100 na koke-koken da ake yi wa alkalan ana gudanar da bincike sannan idan aka same su da laifi za a iya dakatar da su ko kuma a kore su daga aiki.

“Majalisar NJC tana biyan dukkan alkalan tarayya albashinsu, shi ya sa muke samun horo idan aka same su da laifi. NJC kamar kotu ce ga alkalai, saboda masu korafi da alkalai suna wakiltar lauyoyi ne, inda ake tafka muhawara a dukkan wasu batutuwa.

“Bayan sun saurare su, za su yi watsi da bukatar ko kuma su sanya wa alkali takunkumi, ya danganta da hujjar da aka gabatar. Yawancin shari’o’in da ake yi wa alkalan a NJC daga kotun daukaka kara suke tasowa.” In Ji majiyar

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka
Manyan Labarai

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda
Manyan Labarai

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Next Post
FUDMA Za Ta Karrama Sarkin Bichi, Sarkin Daura Da Tsohon Gwamnan Katsina

FUDMA Za Ta Karrama Sarkin Bichi, Sarkin Daura Da Tsohon Gwamnan Katsina

LABARAI MASU NASABA

Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.