• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kano: Alkali Na Fuskantar Tuhuma Kan Kuskuren Da Aka Tafka

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Kano

Yayin da jama’a ke nuna rashin jin dadinsu kan hukuncin da wasu alkalan kotunan daukaka kara suka yi a kan zaben Gwamnan Jihar Kano, majalisar kula da shari’a ta kasa (NJC) ta fara daukan matakai kan wannan lamarin.

Na farko daga cikin alkalan da suke fuskantar tuhuma daga NJC shi ne, mai shari’a Moore Aseimo Abraham Adumein na kotun daukaka kara wanda ya zartar da hukunci mai cike da ce-ce-ku-ce a shari’ar gwamnan Jihar Kano.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Kwamitin Mutum 8 Don Inganta Harkokin Aikin Hajjin 2024
  • Da Dumi-dumi: Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Kujerar Gwamnan Adamawa

LEADERSHIP ta ruwaito cewa mai shari’a Adumein yana fuskantar tuhuma saboda gazawarsa wajen ganowa da kuma kyara kura-kuran rubutun da aka yi a shari’ar Gwamnan Jihar Kano.

Wata majiyar ta ce da yawa daga cikin ‘yan Nijeriya sun yi korafi kan hukuncin shara’ar gwamnan Kano, wanda har yanzu suke bukatar yi musu bayanin yadda aka samu kura-kuran.

“Yawancin ‘yan Nijeriya da ke magana a kan hukuncin ba su karanta ba. Kuskuren da aka samu a hukuncin ya nuna karara kuskure ne na alkali amma ba na yi masa uzuri ba, dole ne ya amsa kuskurensa saboda jahilci ba uzuri ba ne a shari’a, dole ne ya fuskanci hukunci a wuyansa.

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

“Kuskuren wannan hukuncin ya fito ne daga magatakarda wanda ya yi aiki a kai. Alkalin bai karanta karshen hukuncin ba bayan da sakatare ya yi aiki a kai. Alkalin da sakataren da suka yi aiki a kai dole ne su fuskanci hukunci,” in ji majiyar.

Majiyar ta ci gaba da cewa a bangaren shari’a tafka kuskure babban abin kunya ne ba kamar sauran sass aba, shi ya sa kuskure ke zama babban laifi idan an aikata a bangaren.

Ya ce NJC ba ta kare alkalan ta da aka samu da laifin ko kuma kuskure wajen gudanar da aiki. Majiyar ta ce, “Kusan kashi 98 cikin 100 na koke-koken da ake yi wa alkalan ana gudanar da bincike sannan idan aka same su da laifi za a iya dakatar da su ko kuma a kore su daga aiki.

“Majalisar NJC tana biyan dukkan alkalan tarayya albashinsu, shi ya sa muke samun horo idan aka same su da laifi. NJC kamar kotu ce ga alkalai, saboda masu korafi da alkalai suna wakiltar lauyoyi ne, inda ake tafka muhawara a dukkan wasu batutuwa.

“Bayan sun saurare su, za su yi watsi da bukatar ko kuma su sanya wa alkali takunkumi, ya danganta da hujjar da aka gabatar. Yawancin shari’o’in da ake yi wa alkalan a NJC daga kotun daukaka kara suke tasowa.” In Ji majiyar

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
Manyan Labarai

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Next Post
FUDMA Za Ta Karrama Sarkin Bichi, Sarkin Daura Da Tsohon Gwamnan Katsina

FUDMA Za Ta Karrama Sarkin Bichi, Sarkin Daura Da Tsohon Gwamnan Katsina

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.