• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfarawa Na Alfahari Da Sadiya Umar Farouq – Gwamna Matawalle

by Sulaiman
3 years ago
Farouq

Gwamna Bello Muhammed Matawalle na Jihar Zamfara ya bayyana Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, a matsayin nagatartacciyar ‘yar jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne kwanan nan a wajen ƙaddamar da shirin ba da tallafin kuɗi ga mabuƙata, a turance ‘Cash Grant for Vulnerable Groups’ wanda aka yi a zauren majalisa na Gidan Gwamnati a Gusau.

  • Babu Abin Da Zai Kawo Min Cikas Wajen Inganta Rayuwar Jama’a – Sadiya Farou

Gwamna Matawalle ya lissafa alfanun da jihar sa ta samu daga Shirye-Shiryen Inganta Rayuwar Jama’ar Ƙasa (NSIPs), sannan ya yaba wa Ministar da Shugaba Muhammadu Buhari saboda ƙoƙarin su na rage fatara da yunwa a Nijeriya.

Ya ce: “Ministar ta na ta ƙoƙarin tabbatar da cewa ita nagartacciyar ‘ya ce daga jihar mu. Hakan a bayyane ya ke idan an yi la’akari da jerin shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya na agajin jama’a wanda ma’aikatar ta ke aiwatarwa, waɗanda jihar mu ta amfana ƙwarai da gaske daga gare su.

“Haka kuma mun ga haka ta wajen ƙaunar da ta ke nuna wa wannan gwamnatin a kowane lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

“Na fahimci cewa ministar ta zo Jihar Zamfara ne domin ta rarraba kayan abinci da sauran kayayyaki ga ‘yan gudun hijira, kuma ta ƙaddamar da Shirin Ba Da Tallafin Kuɗi ga Mabuƙata, kuma ta raba takardun kama aiki ga ma’aikata ‘yan sa ido masu zaman kan su da aka ɗauka, sannan kuma ta ba da rance maras ruwa ga manoma da mata ‘yan kasuwa.

“Waɗannan abubuwan hoɓɓasa da ake yi wasu muhimman matakai ne da ake ɗauka domin a rage fatara tare da ƙarfafa wa mutanen mu gwiwa ta fuskar tattalin arziki. Halin ƙunci da ake ciki a ƙasar nan ya na buƙatar gwamnatoci a kowane mataki su dage su yi aiki wurjanjan. Wannan ƙoƙarin ya na zuwa ne a matsayin ɗori a kan ƙoƙarin da gwamnatin wannan jihar ke yi ta fuskoki da dama
domin ta sauƙaƙa wa jama’ar wannan jihar.”

A nata jawabin, Minista Sadiya Umar Farouq ta bayyana cewa ma’aikatar ta za ta raba agajin kuɗi ga mabuƙata 4,728 da ke Ƙananan Hukumomi 14 da ke faɗin jihar, yayin da an tantance tare da lissafa mutum 4,616 da za su ci moriyar lamunin Shirin Tallafin Kasuwanci na Gwamnati (wato GEEP) wanda babu ruwa a cikin sa, wanda ya kama daga N50,000 zuwa N300,000.

Ministar ta kuma ƙaddamar da Shirin Faɗakarwa na Ƙasa kan Shirin Ciyar Da Ɗalibai tare da ɗaukar ma’aikata ‘yan sa ido su 130, da sauran ayyuka.

A Jihar Zamfara dai, mutum 800 ne masu cin moriyar waɗanda su ka haɗa da naƙasassu da kuma tsofaffi waɗanda za a ba kyautar N50,000 kowannen su.

Daga bisani, ministar ta ziyarci ɗaya daga cikin sansanonin ‘yan gudun hijira inda ta raba kayan abinci da sauran kayan masarufi, ta kuma ƙaddamar da wani laburare tare da raba kayan cin abinci ga ‘yan makaranta a ƙarƙashin Shirin Ciyar Da ‘Yan Makaranta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
An Nada Muhammad Bin Salman A Matsayin Sabon Firaministan Saudiyya

An Nada Muhammad Bin Salman A Matsayin Sabon Firaministan Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.